• English
  • Business News
Saturday, May 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Ba Abokiyar Gabar Amurka Ba Ce

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin Ba Abokiyar Gabar Amurka Ba Ce
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanakin baya, kwamitocin kula da harkokin diplomasiyya da hada-hadar kudi karkashin majalisar wakilan kasar Amurka sun zartas da wasu shirye-shiryen doka 11 da ke shafar kasar Sin, a yayin da kuma kwamitin musamman mai kula da harkokin takarar Amurka da Sin da majalisar ta kafa ba da jimawa ba, ta gudanar da taron sauraron ra’ayoyin jama’a karo na farko, sai kuma ma’aikatar kula da harkokin wajen Amurka ta zartas da wani shirin da ke da kudin dala miliyan 619 na sayar da makamai da na’urorin soja ga yankin Taiwan na kasar Sin.

Jerin matakan da Amurka ta dauka cike suke da ra’ayoyin yakin cacar baka da ma kiyayya ga kasar Sin, kuma dalilinsu shi ne, don irin ra’ayin da take da shi na cin nasara daga faduwar wani bangare da kuma yadda take daukar kasar Sin a matsayin abokiyar takara mafi kalubale a gare ta. Sai dai daukacin al’ummar Amurka sun san me ke faruwa.

  • An Gudanar Da Bikin Murnar Cika Shekaru 40 Da Kulla Huldar Diplomassiya Tsakanin Sin Da Cote d’Ivoire

A gun taron kwamitin musamman na kula da harkokin takarar Amurka da Sin karkashin majalisar wakilan Amurka, wata ’yar kungiyar CODEPINK mai rajin kare zaman lafiya ta daga allon da ke dauke da rubutun “Sin ba abokiyar gabanmu ba ce”, don bayyana kyamarsu ga yadda majalisar ta gudanar da irin taron. Malama Jodie Evans na daga cikin wadanda suka kafa kungiyar, kuma ta yi nuni da cewa, ganin yadda karfin kasar Sin ke dada karuwa, mahukuntan Amurka suna yada kararaiyi da ma rura kiyayya ga kasar, a kokarin kiyaye babakeren da suka kafa a duniya. Ta ce, “Abin da muke fatan gani shi ne majalisar wakilan Amurka ta gudanar da irin wannan taro kan zaman lafiya da adalci, a maimakon kiyayya da kuma yaki.”

A hakika, ba a rasa samun Amurkawa da ke da irin wannan ra’ayi. Tuni a lokacin gwamnatin Trump, daruruwan masana da ma mutane daga bangarorin siyasa da kasuwanci suka wallafa wata wasika mai taken “Sin ba abokiyar gabar Amurka ba ce” a jaridar Washington Post, don bayyana rashin amincewa da manufofin gwamnati na yin hamayya da kasar Sin. Tsohon shugaban kasar Amurka, Jimmy Carter, wanda ya gane ma idonsa yadda Sin da Amurka suka kulla huldar diplomasiyya, shi ma sau tari ya bayyana cewa, bunkasuwar kasar Sin ba barazana ba ce.

Sai dai mahukuntan kasar Amurka ba su ji muryoyin ba. Don dakile ci gaban kasar Sin, Amurka da sauran kasashen yammacin duniya sun yi ta yada kalaman nan na wai “Sin barazana ce a duniya”. A hakika, kasar Sin ta cimma ci gaba na zo a gani ta fannoni daban daban,amma ko da gaske ne ci gaban kasar na haifar da barazana?

Labarai Masu Nasaba

Firaministan Sin Ya Sauka A Indonesia Domin Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Shugabanci Taro Kan Masana’antu Masu Amfani Da Makamashi Mai Tsafta Da Kare Muhalli 

In mun duba tarihi, tun bayan kafuwar jamhuriyar jama’ar kasar Sin a shekarar 1949, kasar ba ta taba tada yaki ko rikici ba, kuma ba ta taba mallakar yankunan wata kasa ba, har yanzu kasar ta kasance daya tilo a duniya da ta sanya manufar samun ci gaba ta hanyar lumana cikin kundin tsarin mulkinta. Har kullum kasar na martaba ikon mulkin kai da cikakkun yankunan sauran kasashe, kuma ba ta taba tsoma baki cikin harkokin gidan wasu kasashe ba. Kasashen yammacin duniya na ganin cewa, duk kasar da ta samu karfi, za ta kafa babakere da nuna fin karfi, amma hakan ba zai faru ga kasar Sin ba, sakamakon irin ra’ayoyi na “zama lafiya da juna da martaba bambance-bambance” da “zaman lafiya da kasa da kasa” da “kawar da yake-yake a duniya” da ke cikin al’adun gargajiya na tsawon shekaru sama da 5000 na kasar Sin, ra’ayoyin da a zamanin yau aka bayyana su a cikin shawarar kiyaye tsaron duniya da kasar ta gabatar, wato a rika yin shawarwari a maimakon yin fito na fito, kuma a yi hadin gwiwa a maimakon kulla kawance don mayar da wata kasa saniyar ware, da ma cin moriyar juna a maimakon cin nasara daga faduwar wani bangare.

A ganin kasar Sin, tabbatar da ci gaba yana da muhimmanci wurin warware dimbin matsaloli masu wahala da muke fuskanta a duniya, kuma wannan ne dalilin da ya sa kasar Sin ke sa kaimin hadin gwiwar kasa da kasa bisa shawarar ziri daya da hanya daya, tare kuma da gabatar da shawarar raya duniya. Wani hasashen da bankin duniya ya yi ya nuna cewa, idan aka aiwatar da dukkan ayyukan gina ababen more rayuwa ta fannin zirga-zirga bisa shawarar ziri daya da hanya daya, lallai ya zuwa shekarar 2030, shawarar za ta kawo kudin shiga da ya kai dala triliyan 1.6 a kowace shekara, kuma kasashen da suka amsa shawarar ne za su karbi kaso 90% na kudin.

Don haka, muke iya ganin cewa, bunkasuwar kasar Sin dama ce a maimakon kalubale. Kasar Sin na bunkasa kanta ne ba don wata kasa ba ce, ballantana a ce ta maye gurbin wata, abin da take so kawai shi ne, ta kyautata rayuwar al’ummarta.

Kiyaye kyakkyawar hulda tsakanin Sin da Amurka zai taimaka ga kiyaye moriyar kasashen biyu, har ma da kwanciyar hankali da albarka a duniya baki daya. Sin ba abokiyar gabar Amurka ba ce, kamata ya yi a yi watsi da ra’ayin yakin cacar baka da kuma cin nasara daga faduwar wani bangare, don mayar da huldar da ke tsakanin Sin da Amurka kan hanyar da ta kamata. (Lubabatu)

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tafarkin Sin Na Zamanantar Da Kanta Zai Amfani Kasashe Masu Tasowa

Next Post

Mahaifiyar Fitaccen Malamin Addinin Musulunci, Sheikh Gumi, Ta Rasu 

Related

Firaministan Sin Ya Sauka A Indonesia Domin Ziyarar Aiki
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Sauka A Indonesia Domin Ziyarar Aiki

56 minutes ago
Firaministan Sin Ya Shugabanci Taro Kan Masana’antu Masu Amfani Da Makamashi Mai Tsafta Da Kare Muhalli 
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Shugabanci Taro Kan Masana’antu Masu Amfani Da Makamashi Mai Tsafta Da Kare Muhalli 

2 hours ago
CHINADA Ta Nuna Matukar Adawa Da Gasar Wasannin Da Aka Amince Da Kwayoyin Kara Kuzari
Daga Birnin Sin

CHINADA Ta Nuna Matukar Adawa Da Gasar Wasannin Da Aka Amince Da Kwayoyin Kara Kuzari

3 hours ago
Sin Ta Jaddada Da Muhimmancin Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza
Daga Birnin Sin

Sin Ta Jaddada Da Muhimmancin Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza

4 hours ago
An Kaddamar Da Bikin Baje Kolin Aikin Gona Na Kasa Da Kasa Na Cote d’Ivoire
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Bikin Baje Kolin Aikin Gona Na Kasa Da Kasa Na Cote d’Ivoire

5 hours ago
Hunan Ya Ruwaito Samuwar Karin 6.3% Na Kayayyakin Da Ake Fitarwa Zuwa Afirka Tsakanin Janairu Da Afrilu
Daga Birnin Sin

Hunan Ya Ruwaito Samuwar Karin 6.3% Na Kayayyakin Da Ake Fitarwa Zuwa Afirka Tsakanin Janairu Da Afrilu

6 hours ago
Next Post
Mahaifiyar Fitaccen Malamin Addinin Musulunci, Sheikh Gumi, Ta Rasu 

Mahaifiyar Fitaccen Malamin Addinin Musulunci, Sheikh Gumi, Ta Rasu 

LABARAI MASU NASABA

An Gano Kofin Gasar Zakarun Turai Na Mata Bayan Sace Shi Da Aka Yi

An Gano Kofin Gasar Zakarun Turai Na Mata Bayan Sace Shi Da Aka Yi

May 24, 2025
Firaministan Sin Ya Sauka A Indonesia Domin Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Sauka A Indonesia Domin Ziyarar Aiki

May 24, 2025
Tawagar MDD Da Majalisar Shugabancin Libya Sun Kafa Kwamitin Tsagaita Bude Wuta

Tawagar MDD Da Majalisar Shugabancin Libya Sun Kafa Kwamitin Tsagaita Bude Wuta

May 24, 2025
Firaministan Sin Ya Shugabanci Taro Kan Masana’antu Masu Amfani Da Makamashi Mai Tsafta Da Kare Muhalli 

Firaministan Sin Ya Shugabanci Taro Kan Masana’antu Masu Amfani Da Makamashi Mai Tsafta Da Kare Muhalli 

May 24, 2025
Yara Miliyan 2.9 A Nijeriya Ke Fama Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki – UNICEF

Yara Miliyan 2.9 A Nijeriya Ke Fama Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki – UNICEF

May 24, 2025
CHINADA Ta Nuna Matukar Adawa Da Gasar Wasannin Da Aka Amince Da Kwayoyin Kara Kuzari

CHINADA Ta Nuna Matukar Adawa Da Gasar Wasannin Da Aka Amince Da Kwayoyin Kara Kuzari

May 24, 2025

Tsokaci Kan Yadda Wasu Matasa Ke Yin Aure Ba Tare Da Sana’a Ba

May 24, 2025
Sin Ta Jaddada Da Muhimmancin Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza

Sin Ta Jaddada Da Muhimmancin Tsagaita Bude Wuta A Zirin Gaza

May 24, 2025
An Kaddamar Da Bikin Baje Kolin Aikin Gona Na Kasa Da Kasa Na Cote d’Ivoire

An Kaddamar Da Bikin Baje Kolin Aikin Gona Na Kasa Da Kasa Na Cote d’Ivoire

May 24, 2025
Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

May 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.