ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Bai Shirya Yin Gaskiya A Zaɓen 2027 —Buba Galadima

by Sani Anwar
10 months ago
Tinubu

Jigo a jam’iyyar NNPP, Buba Galadima, ya bayyana cewa; ko kaɗan gwamnatin Tinubu ba ta shirya gudanar da sahihin zaɓe a 2027 ba.

Galadima ya bayyana haka ne, a wata hira da aka yi da shi a gidan talabijin na Arise. 

Ya ce, “Wannan gwamanatin, ko kaɗan ba ta shirya gudanar da sahihin zaɓe ba, kamar yadda suke ɓata jam’iyyu; hakan ne yake nuna cewa, ba sa ƙaunar adawa ko kaɗan, musamman idan lokacin zaɓe ya zo”. 

ADVERTISEMENT
  • Tinubu Ya Halarci Ɗaurin Auren Ɗan Yari, Ya Kai Ziyara Gidan Tsohon Shugaban Ƙasa Buhari.
  • Tinubu Ya Ci Amanar Kano, Babu Batun Haɗin Guiwa Tsakaninsa Da Kwankwaso A 2027 – Galadima

A cewar Galadima ana raɗe-raɗin cewa, shugaban ƙasar na shirin naɗa wani ɗan kama-karya a matsayin shugaban hukumar zaɓe ta ƙasa. 

Galadima ya yi matuƙar gargaɗi ga wannan tare da cewa; yin hakan zai iya dagula zaman lafiyar ƙasar ko kuma haifar da wani yaƙin na Basasa. 

LABARAI MASU NASABA

Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta

Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur

Ya ƙara da cewa, “Ina fatan hakan ba gaskiya ba ne, domin kuwa idan wannan mutum ya zama shugaban INEC, ko shakka babu; wannan gwamnati kai tsaye na gayyato yaƙin Basasa ne.”

Da yake mayar da martani a kan batutuwan da jam’iyyun siyasa suka fara yi na yaƙin neman zaɓe, ya zargi hukumar zaɓe ta ƙasa da gazawa waje aiwatar da dokokin yaƙin neman zaɓe.

“Wannan batu na yaƙin neman zaɓe kafin hukumar INEC ta ba shi dama, gwamnatin wancan lokacin ce ta fara yin hakan, wanda kuma hakan ke nuni da cewa; hukumar INEC ba za ta iya yin alƙalanci na gaskiya da adalci ba,” in ji shi, inda ya ƙara da cewa; jam’iyyun adawa sun “Faɗa tarkon” APC ta hanyar shiga yaƙin neman zaɓe da wuri.

Har ila yau, a zaɓen cike gurbi na baya-bayan nan, Galadima ya yi watsi da nasarar da APC ta samu, inda ya yi misali da Jihar Kano da Zamfara, musamman ganin yadda jami’an tsaro suka tsorata masu kaɗa kuri’u”.

Ya ƙara da cewa, “Ba su ci zaɓe ko guda ɗaya ba, amma sun sanar a matsayin su ne waɗanda suka lashe zaɓen. A mazaɓar Bagwai da Shanono, mun samu ƙuri’a 16,000; yayin da APC ta samu ƙuri’a 5,000. A wata ƙaramar hukumar kuma, NNPP ta samu sama da ƙuri’a 5,700, yayin da APC kuma ta samu ƙuri’a 265 kacal.

“Sama da sojoji 30,000 aka kai Zamfara, domin aiwatar da zaɓukan mazaɓu biyar kacal. An yi wa mutane dukan tsiya, an nakasa wasu, an kori wasu, sannan a ƙarshe sun rubuta wa kansu sakamakon zaɓen tare kuma da bayyanawa.”      

 Dangane da irin ƙarfin da jam’iyyar NNPP ke da shi, Galadima ya bayyana cewa; Shugabanta Rabiu Musa Kwankwaso, ba shi da abokin karawa idan ana batu na tasiri a siyasance.

“Kwankwaso shi ne babban jigon siyasar Nijeriya, domin kuwa shi kaɗai ne, wanda tauraronsa yake haskawa; saboda haka, idan har za a yi zaɓe na gaskiya, shi ne mafi farin jini a Nijeriya,” in ji shi. 

Haka zalika, ya yi watsi da rahotannin da ke cewa; Kwankwaso ya gana da shugaba Bola Tinubu kwanan nan.

“Ƙarya ne batun cewa, Kwankwaso ya gana da Tinubu a Faris. Ai wannan cin fuska ne ma, ta yaya za ka yi wa wanda ya ayyana ka a matsayin maƙiyi aiki?” Ya ƙara da cewa, NNPP ta kori waɗanda suka yi iri wannan ta’asa ba tare da amincewar jam’iyyar ba. 

Dangane da ƙawancen siyasa kuma, Galadima ya ce; son kai a tsakanin ƴ an adawa, shi ne musabbabin hana haɗin kai a tsakaninsu.

“Zan so dukkaninmu mu haɗu mu ceci wannan ƙasa tamu baki-ɗaya, amma dukkaninmu, mun san wa da wa ya kamata a tsayar a Nijeriya, domin samun nasarar lashe zaɓe? 

Ya kuma nuna farin cikinsa da batun tattaunawar da aka samu rahoto cewa, ana yi tsakanin tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan da kuma Peter Obi na jam’iyyar Labour Party, inda ya bayyana cewa, “Idan za su iya haɗa kawunansu wuri guda, su fitar da mutum ɗaya; babu shakka ƙasa za ta ɗauki saiti, domin kuwa hakan zai kasance tamkar wata dabara ce ta fitar da mu daga cikin wannan ƙunci da muke ciki.” 

Da yake watsi da batun siyasar yanki da shiyya, Galadima ya ce; “Ban yarda da batun siyasar Arewa da Kudu ba. Mafi cancantar ɗan Nijeriya, ko daga ina ya fito, ko da kuwa daga mafi ƙanƙantar yare ne, shi ya kamata a zaɓa.” 

Galadima ya kuma goyi bayan yawaitar jam’iyyu, yana mai cewa; ko kaɗan bai kyautu a tauye yawansu a Nijeriya ba.

Tinubu
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Gwamnati Ta Amince Da Inganta Cibiyar Kula Da Saran Maciji A Gwambe
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Hukumar NDLEA Ta Lalata Sama Da Tan 12 Na Miyagun Ƙwayoyi A Kano
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

MASU ALAKA

Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta
Manyan Labarai

Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Manyan Labarai

Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur

July 11, 2026
2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa
Da ɗumi-ɗuminsa

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

July 10, 2026
Next Post
Tinubu

Djed Spence: Musulmin Da Ya Fara Bugawa Tawagar Ingila Wasan Ƙwallon Ƙafa A Tarihi

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani

Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
Xi Da Kim Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Yarjejeniyar Abota, Hadin Gwiwa Da Taimakon Juna Tsakanin Sin Da DPRK

Xi Da Kim Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Yarjejeniyar Abota, Hadin Gwiwa Da Taimakon Juna Tsakanin Sin Da DPRK

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina

July 11, 2026
Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
NAF Ta Kai Hare-Haren Sama Kan Maboyar Ƴan Ta’adda A Borno

NAF Ta Kai Hare-Haren Sama Kan Maboyar Ƴan Ta’adda A Borno

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka

July 11, 2026
Gwamna Dauda Ya Raba Buhunan Taki 72,000 Da Kayan Noma Kyauta Ga Manoman Zamfara

Gwamna Dauda Ya Raba Buhunan Taki 72,000 Da Kayan Noma Kyauta Ga Manoman Zamfara

July 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.