• English
  • Business News
Wednesday, June 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Da Afirka Na Da Buri Daya A Wajen Taron G20

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin Da Afirka Na Da Buri Daya A Wajen Taron G20
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ma iya cewa tauraron nahiyar Afirka na haskakawa, a wajen taron kolin kungiyar G20 dake gudana a kasar Brazil, ganin yadda kungiyar kasashen Afirka AU take halartar taron a matsayin mambar kungiyar G20 a karon farko, kana shugaba Bola Tinubu na kasar Najeriya shi ma ya halarci taron bisa gayyatar da aka yi masa. Ban da haka, kasar Brazil mai karbar bakuncin taron tana kokarin daidaita wasu ayyuka tare da kasar Afirka ta Kudu, ganin yadda Afirka ta Kudun za ta zama mai jagorantar kungiyar G20 a karba karba a shekarar 2025 mai zuwa.

 

Hakika yin amfani da dandali na G20 wajen shiga ayyukan kula da al’amuran kasa da kasa ya dace da muradun kasashen Afirka. Saboda cikin Ajandar shekarar 2063 ta kungiyar AU ma, an riga an bayyana burin kungiyar na shiga a dama da ita a karin harkokin kasa da kasa. Sa’an nan a taron G20 na bana, shugaban karba-karba na kungiyar AU, kana shugaban kasar Mauritania, Mohamed Ghazouani, ya yi jawabi, inda ya yi kira da a karfafa hadin gwiwar kasa da kasa, a kokarin raya fasahar noma mai dorewa, da bangaren jin dadin jama’a, da na ilimi, da kayayyakin more rayuwa, don neman cimma burin kawar da yunwa da talauci.

  • Kotu Ta Ɗaure Ɗan TikTok Watanni 32 A Gidan Yari
  • Kotu Ta Wanke Kwamishinan Jigawa Daga Zargin Zina

Ban da haka, a wajen taron G20 na wannan karo, an kimtsa sosai domin taron koli na G20 da zai gudana a kasar Afirka ta Kudu a shekarar 2025. Inda a karkashin taken taron na ”karfafa hadin kai, da daidaituwa, gami da neman ci gaba mai dorewa”, za a fi dora muhimmanci kan matsalolin da suka hada da talauci, da rashin guraben aikin yi, da rashin daidaito a cikin al’umma, da dai sauransu.

 

Labarai Masu Nasaba

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

A zahiri ne, ko a yanzu, ko a nan gaba, kasashen Afirka sun fi bukatar samun ci gaban tattalin arziki, kuma suna neman kare hakkin raya kai na daukacin kasashe masu tasowa, ciki har da kasashen Afirka. Wannan yunkuri ya zama daya da burin kasar Sin.

 

A wajen taron kungiyar G20 na wannan karo, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da jawabi mai taken ”Gina duniya mai adalci da ake iya samun ci gaba na bai daya”, inda ya yi kira ga gamayyar kasa da kasa da su inganta fannonin ciniki, da zuba jari, da hadin gwiwa a kokarin raya kasa, ta yadda karin kasashe masu tasowa za su iya zamanantar da kansu. Ban da haka ya bukaci a nuna goyon baya ga kasashe masu tasowa don su shiga a dama da su ta fuskar raya fasahohin zamani, da na kare muhalli, don neman rage gibin da ake samu tsakanin kasashe masu sukuni da masu tasowa. Haka zalika, a cikin matakai guda 8 na tallafawa kokarin raya duniya, da kasar Sin ta dauka, wadanda shugaba Xi na kasar Sin ya ambata a ciki jawabinsa, akwai ”Taimaki kasashen Afirka a kokarinsu na raya kansu” da ”Yafe wa kasashe marasa karfin tattalin arziki da suka kulla hulda da Sin harajin kwastam kan dukkan kayayyakin da suke neman sayarwa a kasuwannin Sin”, gami da ”kaddamar da shawarar hadin gwiwa a fannin kimiyya da fasaha cikin ‘yanci, don baiwa kasashe masu tasowa damar more sabbin fasahohin da aka kirkira a duniya”, da dai makamantansu.

 

Duk a wajen taron wannan karo, shugaba Xi na kasar Sin ya yi wani jawabi kan batun yin gyare-gyare kan tsarin kula da harkokin kasa da kasa, inda ya ce ya kamata a kara yafe wa kasashe masu tasowa bashin da ake bin su, ko kuma tsawaita wa’adin biyan bashin. Ya kuma jaddada bukatar kara wakilcin kasashe masu tasowa a fannin kula da ayyukan hada-hadar kudi, da bukatar kasashe masu sukuni da su magance gyara manufofinsu na kudi yadda suka ga dama, tare da haifar da mummunan tasiri kan tattalin arzikin sauran kasashe.

 

Watakila za ka so ka yi tambaya cewa, ina dalilin da ya sa kasar Sin ke son ganin ci gaban tattalin arzikin kasashe masu tasowa? Hakika dalili shi ne tunanin kasar a fannin hulda da sauran kasashe, na gina al’ummar dan Adam mai kyakkyawar makoma. A ganin Sinawa, ci gaban tattalin arizkin sauran kasashe shi ma zai amfani kasar Sin. Saboda haka shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya ce kasar Sin na son hadin gwiwa tare da sauran kasashe masu tasowa a kokarin samun zamanantarwa ta bai daya. Ya kuma yi amfani da misalin Sin na fitar da jama’arta miliyan 800 daga kangin talauci wajen karfafa gwiwar kasashe daban daban, inda ya ce, ”Kasar Sin ta cimma nasara a wannan fanni, sauran kasashe masu tasowa su ma za su iya tabbatar da hakan.” (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Ɗaure Ɗan TikTok Watanni 32 A Gidan Yari

Next Post

Babu Wata Kasa Da Za Ta Ce ”Ita Kadai Ta Isa Gayya”

Related

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?
Daga Birnin Sin

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

6 hours ago
Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

8 hours ago
Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba
Daga Birnin Sin

Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

9 hours ago
Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu
Daga Birnin Sin

Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu

12 hours ago
Sabuwar Shugabar Kwamitin Wasannin Olympics Na Duniya Na Fatan Sake Ziyartar Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Sabuwar Shugabar Kwamitin Wasannin Olympics Na Duniya Na Fatan Sake Ziyartar Kasar Sin

19 hours ago
Xi Jinping Zai Halarci Bikin Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan Da Yakin Kin Tafarkin Murdiya
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Zai Halarci Bikin Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan Da Yakin Kin Tafarkin Murdiya

20 hours ago
Next Post
Babu Wata Kasa Da Za Ta Ce ”Ita Kadai Ta Isa Gayya”

Babu Wata Kasa Da Za Ta Ce ''Ita Kadai Ta Isa Gayya''

LABARAI MASU NASABA

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?

June 24, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

June 24, 2025
Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

June 24, 2025
Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

June 24, 2025
Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

June 24, 2025
Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

June 24, 2025
Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

June 24, 2025
Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu

Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu

June 24, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisar Dattawa Ta Kara Tsawaita Aiwatar Da Ayyukan Kasafin Kudi Na 2024 Da Wata 6

June 24, 2025
Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

June 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.