Mamban ofishin siyasa na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, kana ministan harkokin wajen kasar Wang Yi, da shugaban kasar Kiribati, kuma ministan harkokin wajen kasar Taneti Maamau, sun jagoranci taron ministocin harkokin wajen kasar Sin da kasashen yankin Pasifik karo na uku a birnin Xiamen dake kudu maso gabashin kasar Sin.
A yayin taron, Wang Yi ya gabatar da shawarwari guda shida kan kafa kyakkyawar makomar bai daya ta Sin da kasashen yankin Pasifik. Na farko shi ne dagewa kan mutunta juna. Ya ce kasar Sin tana goyon bayan kasashen yankin wajen kiyaye cikakken ’yancinsu, tsaro da muradunsu na ci gaban. Kuma Sin ta yi imanin cewa, kasashen yankin za su ci gaba da bin manufar kasancewar kasar Sin daya tilo a duniya. Na biyu shi ne tsayawa tsayin daka kan sanya neman ci gaba a gaban kome. Ya ce bangarorin biyu za su aiwatar da shawarar ci gaban duniya tare da zurfafa hadin gwiwa kan raya shawarar “Ziri daya da hanya daya” mai inganci, kana da gaggauta inganta shawarwari game da cimma yarjejeniyar cinikayya cikin ’yanci a tsakaninsu. Na uku shi ne, a dora muhimmanci kan muradun jama’a. Bisa ga haka, za a gudanar da wasu kananan ayyuka masu halin musamman da inganci guda 200 da suka shafi zaman rayuwar jama’a. Na hudu shi ne dagewa kan musayar ra’ayi da koyi da juna, ciki har da karfafa mu’amala tsakanin kafofin watsa labarai, matasa, mata, harkokin wasanni, da dai sauransu. Na biyar shi ne kiyaye adalci. Ya ce kamata ya yi a tsaya kan kare tsarin kasa da kasa bisa tushen dokokin kasa da kasa, da daukar Majalisar Dinkin Duniya a matsayin ginshikinsa. Na shida shi ne, a zama tsintsiya madaurinki guda. Ya ce kasar Sin na son karfafa hadin gwiwa da kasashen yankin Pasifik wajen tinkarar sauyin yanayi, wanda duk duniya ke fuskanta. (Mai fassara: Bilkisu Xin)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp