• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Na Ba Da Gudummawa Ta Fuskar Ingiza Zamanantar Da Duniya

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin Na Ba Da Gudummawa Ta Fuskar Ingiza Zamanantar Da Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da duniya ke ci gaba da fuskantar manyan kalubale daga sassa daban daban, masharhanta na ganin wannan lokaci ne da ya dace sassan kasa da kasa su kara azamar bullo da dabarun hadin gwiwa, na tsame duniya daga mawuyacin halin koma bayan tattalin arziki da zamantakewa da take ciki.

Kaza lika, lokaci ya yi da duniya za ta rungumi matakan wanzar da zaman lafiya, da samar da ci gaban bai daya, domin cin gajiyar dukkanin al’ummun kasa da kasa. Hakan ne kuma ya sa har kullum kasar Sin ke sahun gaba a wannan fage. Idan mun lura da matakan da Sin ke dauka na baiwa ci gaban duniya gudummawa, za mu gamsu cewa matakai ne masu fa’ida ta kyakkyawan tasiri, ta yadda har kullum Sin din ke aiki tukuru, kuma kafada da kafada da sauran sassan duniya, wajen ganin an cimma burin zamanantar da al’amura, da samar da ci gaba cikin lumana, da aiwatar da matakan hadin gwiwa na bai daya.

  • Wang Yi: Sin Da Angola Sun Kafa Misali Na Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa 
  • Xi Ya Gana Da Shugaban Hukumar Gudanarwar Turai Da Shugabar Kungiyar EU

Sanin kowa ne cewa, duniya gida ne guda na daukacin bil Adama, kuma wuri na cin gajiyar daukacin al’ummun kasashen duniya, don haka kamata ya yi sassan kasa da kasa su kara kokarin yin hadin gwiwa, wajen shawo kan kalubalen dake addabar duniya, su goyi bayan matakan bunkasa duniya na bai daya, da inganta moriyar jama’a baki daya.

Idan muka yi la’akari da ci gaban da kasar Sin ke samu ta fuskar zamanantar da kasa, da fadada bude kofa bisa babban matsayi, da ma yadda kasar ke kara azamar bunkasa ci gaba mai inganci, za mu fahimci sirrin dake cikin damammaki da kasar ke samarwa, wajen ingiza ci gaban duniya.

Tsarin zamanantar da kasa na Sin, yana ci gaba da ingiza bunkasar tattalin arzikin duniya, kuma sabanin makamantansa da ake aiwatarwa a yanukunan yammacin duniya, salon kasar Sin na bayar da damar samun ci gaban bai daya. Tuni kasar Sin ta cimma manyan nasarori a fannin yaki da fatara, da kyautata rayuwar al’ummarta. Bisa hakan, muna iya cewa, salon zamanantarwa na Sin ya dace da burin daukacin bil Adama na samun ingantacciyar rayuwa.

Labarai Masu Nasaba

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yayin da Sin ke shiga sabon mataki na ci gaba mai inganci, kofofin takara mai tsafta suna kara budewa, kuma tsarin kasar na bude kofa ga kowa, da ingiza ci gaban bai daya, da gudummawarta a fannin gina budadden tsarin tattalin arzikin duniya, kyakkyawan labari ne ga duniya da a yanzu ke fama da tafiyar hawainiya a fannin na tattalin arziki.

Fatan dai shi ne duniya ta kara fahimtar kasar Sin, a matsayinta na abokiyar tafiya, ba wai barazana ko abokiyar hamayyar ko wane bangare ba. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaSinTaipei
ShareTweetSendShare
Previous Post

Masu Bincike: Babu Wata Shaida Da Ta Nuna Cewa An Tilastawa Ma’aikata Yin Aiki A Kamfanin Volkswagen Na Xinjiang

Next Post

Shettima Ya Ziyarci Wadanda Sojoji Suka Jefawa Bam A Kaduna

Related

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

15 hours ago
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata
Daga Birnin Sin

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

16 hours ago
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

18 hours ago
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya
Daga Birnin Sin

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

19 hours ago
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

1 day ago
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

1 day ago
Next Post
Shettima Ya Ziyarci Wadanda Sojoji Suka Jefawa Bam A Kaduna

Shettima Ya Ziyarci Wadanda Sojoji Suka Jefawa Bam A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.