• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Na Ba Da Gudummawa Ta Fuskar Ingiza Zamanantar Da Duniya

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin Na Ba Da Gudummawa Ta Fuskar Ingiza Zamanantar Da Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da duniya ke ci gaba da fuskantar manyan kalubale daga sassa daban daban, masharhanta na ganin wannan lokaci ne da ya dace sassan kasa da kasa su kara azamar bullo da dabarun hadin gwiwa, na tsame duniya daga mawuyacin halin koma bayan tattalin arziki da zamantakewa da take ciki.

Kaza lika, lokaci ya yi da duniya za ta rungumi matakan wanzar da zaman lafiya, da samar da ci gaban bai daya, domin cin gajiyar dukkanin al’ummun kasa da kasa. Hakan ne kuma ya sa har kullum kasar Sin ke sahun gaba a wannan fage. Idan mun lura da matakan da Sin ke dauka na baiwa ci gaban duniya gudummawa, za mu gamsu cewa matakai ne masu fa’ida ta kyakkyawan tasiri, ta yadda har kullum Sin din ke aiki tukuru, kuma kafada da kafada da sauran sassan duniya, wajen ganin an cimma burin zamanantar da al’amura, da samar da ci gaba cikin lumana, da aiwatar da matakan hadin gwiwa na bai daya.

  • Wang Yi: Sin Da Angola Sun Kafa Misali Na Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa 
  • Xi Ya Gana Da Shugaban Hukumar Gudanarwar Turai Da Shugabar Kungiyar EU

Sanin kowa ne cewa, duniya gida ne guda na daukacin bil Adama, kuma wuri na cin gajiyar daukacin al’ummun kasashen duniya, don haka kamata ya yi sassan kasa da kasa su kara kokarin yin hadin gwiwa, wajen shawo kan kalubalen dake addabar duniya, su goyi bayan matakan bunkasa duniya na bai daya, da inganta moriyar jama’a baki daya.

Idan muka yi la’akari da ci gaban da kasar Sin ke samu ta fuskar zamanantar da kasa, da fadada bude kofa bisa babban matsayi, da ma yadda kasar ke kara azamar bunkasa ci gaba mai inganci, za mu fahimci sirrin dake cikin damammaki da kasar ke samarwa, wajen ingiza ci gaban duniya.

Tsarin zamanantar da kasa na Sin, yana ci gaba da ingiza bunkasar tattalin arzikin duniya, kuma sabanin makamantansa da ake aiwatarwa a yanukunan yammacin duniya, salon kasar Sin na bayar da damar samun ci gaban bai daya. Tuni kasar Sin ta cimma manyan nasarori a fannin yaki da fatara, da kyautata rayuwar al’ummarta. Bisa hakan, muna iya cewa, salon zamanantarwa na Sin ya dace da burin daukacin bil Adama na samun ingantacciyar rayuwa.

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Yayin da Sin ke shiga sabon mataki na ci gaba mai inganci, kofofin takara mai tsafta suna kara budewa, kuma tsarin kasar na bude kofa ga kowa, da ingiza ci gaban bai daya, da gudummawarta a fannin gina budadden tsarin tattalin arzikin duniya, kyakkyawan labari ne ga duniya da a yanzu ke fama da tafiyar hawainiya a fannin na tattalin arziki.

Fatan dai shi ne duniya ta kara fahimtar kasar Sin, a matsayinta na abokiyar tafiya, ba wai barazana ko abokiyar hamayyar ko wane bangare ba. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaSinTaipei
ShareTweetSendShare
Previous Post

Masu Bincike: Babu Wata Shaida Da Ta Nuna Cewa An Tilastawa Ma’aikata Yin Aiki A Kamfanin Volkswagen Na Xinjiang

Next Post

Shettima Ya Ziyarci Wadanda Sojoji Suka Jefawa Bam A Kaduna

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

15 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

15 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

17 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

20 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

21 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

22 hours ago
Next Post
Shettima Ya Ziyarci Wadanda Sojoji Suka Jefawa Bam A Kaduna

Shettima Ya Ziyarci Wadanda Sojoji Suka Jefawa Bam A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.