Rahotanni sun bayyana cewa, kasashen Rasha, da Sin da Pakistan, sun gabatar da wani daftarin kudurin kwamitin sulhun MDD, kan halin da ake ciki a Iran. Game da hakan, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun, ya shaidawa nuni taron manema labarai da aka saba yi a yau Litinin cewa, harin da Amurka ta kai kan wuraren da kasar Iran ta girke na’urorin nukiliya ya saba wa manufar tsarin dokokin MDD, tare da kara ta’azzara tashin hankali a yankin gabas ta tsakiya, don haka, dole ne kwamitin sulhun ya dauki mataki kan batun.
Kakakin ya kara da cewa, kasar Sin na sa ran mambobin kwamitin za su goyi bayan daftarin kudurin, tare da sa kaimin kwamitin ya taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da zaman lafiya, da tsaron kasa da kasa.
- ‘Yan Bindiga Sun Sace Dukkan Fasinjojin Motar Bas A Jihar Benuwe
- Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi
Dangane da goyon bayan da majalisar dokokin Iran ta nuna game da rufe mashigin tekun Hormuz, mashigin tekun Farisa, da yankin ruwan da ke kewaye da shi muhimmiyar hanyar cinikayyar kayayyaki da makamashi ce ta kasa da kasa. Kuma kasar Sin ta yi kira ga kasashen duniya da su kara kokarin sa kaimi ga kwantar da kurar rikici, don magance karin tasiri da tashin hankalin da ake fuskanta a shiyyar ka iya haifarwa ga gaban tattalin arzikin duniya.
Baya ga haka kuma, kakakin ya bayyana cewa, ‘yan kasar Sin 3,125 sun riga sun fice daga kasar Iran lami lafiya, kuma ofishin jakadancin kasar Sin dake Isra’ila, ya taimaka wa ‘yan kasar Sin sama da 500 barin Isra’ila yadda ya kamata, kana ya taimaka wa wasu ‘yan kasar Birtaniya, da Indiya, da Poland wajen barin kasar lami lafiya. (Mai fassara Bilkisu Xin)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp