Kwararren masananin tattalin arziki na kasar Madagascar Claudio Rabenja, ya ce kasar Sin ta yi rawar gani wajen wanzar da ci gaban masana’antun nahiyar Afirka, ta yadda suka kai matsayin dunkulewa da tsarin samar da hajoji na duniya baki daya.
Claudio Rabenja, ya bayyana hakan ne yayin wata zantawa da wakilin kamfanin dillancin labarai na Sin wato Xinhua a kwanan nan. Masananin ya jinjinawa tallafin kasar Sin ga nahiyar Afirka, a fannonin samar da ababen more rayuwa ta fuskar cinikayya, wadanda suka hada da yankunan masana’antu, da cibiyoyin bunkasa tattalin arziki, da dandalolin samar da hidimomi, ta yadda kasuwannin Afirka za su kara hadewa da sauran takwarorinsu na kasa da kasa ta fuskar sarrafa abubuwan bukatun masana’antu a gida, wanda hakan muhimmin mataki ne na wanzar da ci gaban masana’antun nahiyar.
Kazalika, masananin ya jinjinawa tsarin hadin gwiwar Sin da nahiyar Afirka karkashin tsarin hadin kan kasashe masu tasowa, wanda aka gina bisa salon daidaiton musaya tsakanin kasashe masu tasowa, sabanin salon “kashin dankali” da aka gani yayin mulkin mallaka da ya shude.
Alkaluman kididdiga sun nuna cewa a shekarar 2024, alakar cinikayya tsakanin Sin da kasashen Afirka ta kai darajar dalar Amurka biliyan 295.6, adadin da ya karu da kaso 4.8 bisa dari a mizanin shekara-shekara. Yayin da har zuwa karshen shekarar 2024, Sin ta ci gaba da kasancewa abokiyar huldar cinikayyar Afirka mafi girma a duniya cikin shekaru 16 a jere. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp