ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Na Taka Rawar Gani Wajen Raba Fasahohinta Na Bunkasa Tattalin Arziki Na Zamani Da Sauran Kasashe Masu Tasowa

by CGTN Hausa
2 years ago
Sin

A shekarun baya bayan nan, musamman a lokacin da ake fama da tafiyar hawainiya a fannin raya tattalin arzikin duniya, karin kasashe masu tasowa, ciki har da na nahiyar Afirka, suna mayar da hankali ga muhimmancin raya fannin tattalin arziki na dijital, wato sassan tattalin arziki da ake rayawa ta amfani da fasahohin sadarwa.

A kasar Sin wannan fanni ne da ya samu matukar ci gaba, wanda kuma a baya bayan nan kasar ta karkashin kamfanonin ta masu kwarewar fasahohi, ke shigar da fasahohinsu na dijital cikin sassan kasashen nahiyar Afirka, ta yadda nahiyar ke samun karin dunkulewa da juna, da ma sauran sassan duniya. A hannu guda kuma, kasashen nahiyar sun fara cin gajiya daga tarin alfanun dake tattare da dabarun raya wannan fanni na tattalin arziki.

  • Xi Ya Yi Musayar Sakon Taya Murna Da Takwaransa Na Kenya Kan Cika Shekaru 60 Da Kulla Huldar Diplomasiyya Tsakanin Sin Da Kenya
  • Sin Ta Gudanar Da Bikin Tunawa Da Wadanda Aka Halaka A Birnin Nanjing

Sanin kowa ne cewa, gina fannin tattalin arziki na dijital, hanya ce ta cimma moriya mai tarin yawa a kasuwanni da cibiyoyin hada-hadar kudi, kuma kasashe masu tasowa ciki har da na Afirka, na da ikon samun kaso mai tsoka daga dunkulewar duniya waje guda da fannin ke haifarwa.

ADVERTISEMENT

Kamar dai kasar Sin, su ma kasashen Afirka na da babbar kasuwa ta cinikayyar hajoji, da matasa dake cikin lokutan kwadago, don haka dabarun kasar Sin na raya tattalin arziki na zamani, a fannin hada-hadar kudade, da inshora, da sayayyar kayayyakin bukata na yau da kullum, da dunkule sassan kasuwanni, za su ci gaba da amfanar kasashen Afirka yadda ya kamata.

Sai dai duk da tarin alfanun wannan fanni, kasashen Afirka na da babban gibi, kafin su kai ga matsayin cin gajiyar tattalin arziki na dijital yadda ya kamata, sakamakon karancin manyan ababen more rayuwa, da karancin kwarewa ta ilimin da ake bukata domin sarrafa naurori masu nasaba.

LABARAI MASU NASABA

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

Masharhanta na ganin idan har nahiyar Afirka ta kai ga shawo kan wadannan matsaloli, to hakan zai ba ta damar cike gibi, da ratar da sauran sassan duniya masu ci gaba suka ba ta. Kuma albarkacin shigar kamfanonin fasahohin sadarwa na Sin irin su Huawei, da sauransu, wadanda ke samar da manyan fasahohin sadarwa, kamar manyan turakun yanar gizo, da sauran fasahohi masu nasaba, sannu a hankali Afirka za ta kai ga cimma nasarorin da ake fata.

Don haka babban buri a nan shi ne, dorewar hulda mai kyau tsakanin Sin da kasashen Afirka, a fannonin wanzar da ci gaba, ciki har da wannan muhimmin fanni na raya tattalin arziki na dijital, wato wanda ake gudanarwa ta amfani da naurorin zamani.(Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci
Daga Birnin Sin

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

November 15, 2025
Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo
Daga Birnin Sin

Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

November 15, 2025
An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka
Daga Birnin Sin

An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

November 15, 2025
Next Post
Ministan Wajen Angola: Manyan Ababen More Rayuwa Da Kamfanonin Sin Suka Gina A Kasar Angola Sun Inganta Ci Gaban Kasar

Ministan Wajen Angola: Manyan Ababen More Rayuwa Da Kamfanonin Sin Suka Gina A Kasar Angola Sun Inganta Ci Gaban Kasar

LABARAI MASU NASABA

Za A Yi Gwanjon Rigunan Messi Na Gasar Kofin Duniya Ta 2022 Da Kudi Tsagwagwa

Ina Son Kasancewa Cikin Koshin Lafiya Kafin Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Messi

November 15, 2025
Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

November 15, 2025
Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

November 15, 2025
Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

Sin Ta Sha Alwashin Bunkasa Goyon Bayan Juna Tsakaninta Da Saliyo

November 15, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

An Gabatar Da Sabuwar Hanyar Raya Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Tsakanin Sin Da Afirka

November 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Yi Taka-tsantsan Da Batun Yankin Taiwan 

November 15, 2025
Illolin Neman Kudi Ido Rufe Ba Tare Da Kula Da Halal Ko Haram Ba

Illolin Neman Kudi Ido Rufe Ba Tare Da Kula Da Halal Ko Haram Ba

November 15, 2025
Jakadan Sin A Japan Ya Bayyana Matukar Adawa Da Kalaman Firaminista Takaichi Dangane Da Kasar Sin

Jakadan Sin A Japan Ya Bayyana Matukar Adawa Da Kalaman Firaminista Takaichi Dangane Da Kasar Sin

November 15, 2025
Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.