• English
  • Business News
Sunday, July 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Na Taka Rawar Gani Wajen Raba Fasahohinta Na Bunkasa Tattalin Arziki Na Zamani Da Sauran Kasashe Masu Tasowa

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin Na Taka Rawar Gani Wajen Raba Fasahohinta Na Bunkasa Tattalin Arziki Na Zamani Da Sauran Kasashe Masu Tasowa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A shekarun baya bayan nan, musamman a lokacin da ake fama da tafiyar hawainiya a fannin raya tattalin arzikin duniya, karin kasashe masu tasowa, ciki har da na nahiyar Afirka, suna mayar da hankali ga muhimmancin raya fannin tattalin arziki na dijital, wato sassan tattalin arziki da ake rayawa ta amfani da fasahohin sadarwa.

A kasar Sin wannan fanni ne da ya samu matukar ci gaba, wanda kuma a baya bayan nan kasar ta karkashin kamfanonin ta masu kwarewar fasahohi, ke shigar da fasahohinsu na dijital cikin sassan kasashen nahiyar Afirka, ta yadda nahiyar ke samun karin dunkulewa da juna, da ma sauran sassan duniya. A hannu guda kuma, kasashen nahiyar sun fara cin gajiya daga tarin alfanun dake tattare da dabarun raya wannan fanni na tattalin arziki.

  • Xi Ya Yi Musayar Sakon Taya Murna Da Takwaransa Na Kenya Kan Cika Shekaru 60 Da Kulla Huldar Diplomasiyya Tsakanin Sin Da Kenya
  • Sin Ta Gudanar Da Bikin Tunawa Da Wadanda Aka Halaka A Birnin Nanjing

Sanin kowa ne cewa, gina fannin tattalin arziki na dijital, hanya ce ta cimma moriya mai tarin yawa a kasuwanni da cibiyoyin hada-hadar kudi, kuma kasashe masu tasowa ciki har da na Afirka, na da ikon samun kaso mai tsoka daga dunkulewar duniya waje guda da fannin ke haifarwa.

Kamar dai kasar Sin, su ma kasashen Afirka na da babbar kasuwa ta cinikayyar hajoji, da matasa dake cikin lokutan kwadago, don haka dabarun kasar Sin na raya tattalin arziki na zamani, a fannin hada-hadar kudade, da inshora, da sayayyar kayayyakin bukata na yau da kullum, da dunkule sassan kasuwanni, za su ci gaba da amfanar kasashen Afirka yadda ya kamata.

Sai dai duk da tarin alfanun wannan fanni, kasashen Afirka na da babban gibi, kafin su kai ga matsayin cin gajiyar tattalin arziki na dijital yadda ya kamata, sakamakon karancin manyan ababen more rayuwa, da karancin kwarewa ta ilimin da ake bukata domin sarrafa naurori masu nasaba.

Labarai Masu Nasaba

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Aiwatar Da Manyan Ayyukan Kasa Cikin Inganci

An Yi Taron Farko Na Shugabannin Matasa Na Dandalin Zaman Lafiya Da Tsaro Na Sin Da Afirka

Masharhanta na ganin idan har nahiyar Afirka ta kai ga shawo kan wadannan matsaloli, to hakan zai ba ta damar cike gibi, da ratar da sauran sassan duniya masu ci gaba suka ba ta. Kuma albarkacin shigar kamfanonin fasahohin sadarwa na Sin irin su Huawei, da sauransu, wadanda ke samar da manyan fasahohin sadarwa, kamar manyan turakun yanar gizo, da sauran fasahohi masu nasaba, sannu a hankali Afirka za ta kai ga cimma nasarorin da ake fata.

Don haka babban buri a nan shi ne, dorewar hulda mai kyau tsakanin Sin da kasashen Afirka, a fannonin wanzar da ci gaba, ciki har da wannan muhimmin fanni na raya tattalin arziki na dijital, wato wanda ake gudanarwa ta amfani da naurorin zamani.(Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GazaHamasKasar Sin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Taron Raya Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Kara Shaida Muhimmancin Zuba Jari A Kasar

Next Post

Ministan Wajen Angola: Manyan Ababen More Rayuwa Da Kamfanonin Sin Suka Gina A Kasar Angola Sun Inganta Ci Gaban Kasar

Related

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Aiwatar Da Manyan Ayyukan Kasa Cikin Inganci
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Aiwatar Da Manyan Ayyukan Kasa Cikin Inganci

10 minutes ago
An Yi Taron Farko Na Shugabannin Matasa Na Dandalin Zaman Lafiya Da Tsaro Na Sin Da Afirka
Daga Birnin Sin

An Yi Taron Farko Na Shugabannin Matasa Na Dandalin Zaman Lafiya Da Tsaro Na Sin Da Afirka

19 hours ago
Kasar Sin Ta Ba Da Rahoton Samun Ci Gaban Aikin Gona Mara Gurbata Muhalli Ba Tare Da Tangarda Ba
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Ba Da Rahoton Samun Ci Gaban Aikin Gona Mara Gurbata Muhalli Ba Tare Da Tangarda Ba

20 hours ago
Xia Xueying: Muna Sayo Kashi 90% Na Kayan Aikinmu Daga Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Xia Xueying: Muna Sayo Kashi 90% Na Kayan Aikinmu Daga Kasar Sin

21 hours ago
Wakilin Sin: Hukumar Shiga Tsakani Ta Duniya Za Ta Karfafa Warware Takaddamar Kasa Da Kasa Cikin Lumana
Daga Birnin Sin

Wakilin Sin: Hukumar Shiga Tsakani Ta Duniya Za Ta Karfafa Warware Takaddamar Kasa Da Kasa Cikin Lumana

22 hours ago
Xi Da Takwaransa Na Mauritania Ghazouani Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 60 Da Kulla Huldar Diflomasiyya
Daga Birnin Sin

Xi Da Takwaransa Na Mauritania Ghazouani Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 60 Da Kulla Huldar Diflomasiyya

23 hours ago
Next Post
Ministan Wajen Angola: Manyan Ababen More Rayuwa Da Kamfanonin Sin Suka Gina A Kasar Angola Sun Inganta Ci Gaban Kasar

Ministan Wajen Angola: Manyan Ababen More Rayuwa Da Kamfanonin Sin Suka Gina A Kasar Angola Sun Inganta Ci Gaban Kasar

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Aiwatar Da Manyan Ayyukan Kasa Cikin Inganci

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Aiwatar Da Manyan Ayyukan Kasa Cikin Inganci

July 20, 2025
Mutane 2 Sun Gurfana Gaban Alƙali Kan Sare Bishiya Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano

Mutane 2 Sun Gurfana Gaban Alƙali Kan Sare Bishiya Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano

July 20, 2025
Bayan Shekaru 7 Yana Ɓoye, NDLEA Ta Cafke Babban Dillalin Ƙwayoyi

Bayan Shekaru 7 Yana Ɓoye, NDLEA Ta Cafke Babban Dillalin Ƙwayoyi

July 20, 2025
Yanzu Haka Muna Bincikar Gwamnoni 18 – Shugaban EFCC

Yanzu Haka Muna Bincikar Gwamnoni 18 – Shugaban EFCC

July 20, 2025
Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Zama Sakatariyar Kungiyar Yaƙi Da Cutar Daji

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Zama Sakatariyar Kungiyar Yaƙi Da Cutar Daji

July 20, 2025
Ki Bar Auna Yadda Mijinki Yake Miki Da Yadda Wani Yake Wa Matarsa

Ki Bar Auna Yadda Mijinki Yake Miki Da Yadda Wani Yake Wa Matarsa

July 20, 2025
Ko Kin San… Yadda Ake Magance Cutar Sanyi Ga Ma’aurata (Infection)

Ko Kin San… Yadda Ake Magance Cutar Sanyi Ga Ma’aurata (Infection)

July 20, 2025
Bayan Shekaru 20 Yana Bacci, Yariman Saudiyya Ya Rasu

Bayan Shekaru 20 Yana Bacci, Yariman Saudiyya Ya Rasu

July 20, 2025
Amfanin Kabewa A Jikin Mace

Amfanin Kabewa A Jikin Mace

July 20, 2025
Matsalolin Da Ke Tattare Da Zawarci Da Rashin Yin Aure Da Wuri

Matsalolin Da Ke Tattare Da Zawarci Da Rashin Yin Aure Da Wuri

July 20, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.