• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Na Taka Rawar Gani Wajen Raba Fasahohinta Na Bunkasa Tattalin Arziki Na Zamani Da Sauran Kasashe Masu Tasowa

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin Na Taka Rawar Gani Wajen Raba Fasahohinta Na Bunkasa Tattalin Arziki Na Zamani Da Sauran Kasashe Masu Tasowa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A shekarun baya bayan nan, musamman a lokacin da ake fama da tafiyar hawainiya a fannin raya tattalin arzikin duniya, karin kasashe masu tasowa, ciki har da na nahiyar Afirka, suna mayar da hankali ga muhimmancin raya fannin tattalin arziki na dijital, wato sassan tattalin arziki da ake rayawa ta amfani da fasahohin sadarwa.

A kasar Sin wannan fanni ne da ya samu matukar ci gaba, wanda kuma a baya bayan nan kasar ta karkashin kamfanonin ta masu kwarewar fasahohi, ke shigar da fasahohinsu na dijital cikin sassan kasashen nahiyar Afirka, ta yadda nahiyar ke samun karin dunkulewa da juna, da ma sauran sassan duniya. A hannu guda kuma, kasashen nahiyar sun fara cin gajiya daga tarin alfanun dake tattare da dabarun raya wannan fanni na tattalin arziki.

  • Xi Ya Yi Musayar Sakon Taya Murna Da Takwaransa Na Kenya Kan Cika Shekaru 60 Da Kulla Huldar Diplomasiyya Tsakanin Sin Da Kenya
  • Sin Ta Gudanar Da Bikin Tunawa Da Wadanda Aka Halaka A Birnin Nanjing

Sanin kowa ne cewa, gina fannin tattalin arziki na dijital, hanya ce ta cimma moriya mai tarin yawa a kasuwanni da cibiyoyin hada-hadar kudi, kuma kasashe masu tasowa ciki har da na Afirka, na da ikon samun kaso mai tsoka daga dunkulewar duniya waje guda da fannin ke haifarwa.

Kamar dai kasar Sin, su ma kasashen Afirka na da babbar kasuwa ta cinikayyar hajoji, da matasa dake cikin lokutan kwadago, don haka dabarun kasar Sin na raya tattalin arziki na zamani, a fannin hada-hadar kudade, da inshora, da sayayyar kayayyakin bukata na yau da kullum, da dunkule sassan kasuwanni, za su ci gaba da amfanar kasashen Afirka yadda ya kamata.

Sai dai duk da tarin alfanun wannan fanni, kasashen Afirka na da babban gibi, kafin su kai ga matsayin cin gajiyar tattalin arziki na dijital yadda ya kamata, sakamakon karancin manyan ababen more rayuwa, da karancin kwarewa ta ilimin da ake bukata domin sarrafa naurori masu nasaba.

Labarai Masu Nasaba

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Masharhanta na ganin idan har nahiyar Afirka ta kai ga shawo kan wadannan matsaloli, to hakan zai ba ta damar cike gibi, da ratar da sauran sassan duniya masu ci gaba suka ba ta. Kuma albarkacin shigar kamfanonin fasahohin sadarwa na Sin irin su Huawei, da sauransu, wadanda ke samar da manyan fasahohin sadarwa, kamar manyan turakun yanar gizo, da sauran fasahohi masu nasaba, sannu a hankali Afirka za ta kai ga cimma nasarorin da ake fata.

Don haka babban buri a nan shi ne, dorewar hulda mai kyau tsakanin Sin da kasashen Afirka, a fannonin wanzar da ci gaba, ciki har da wannan muhimmin fanni na raya tattalin arziki na dijital, wato wanda ake gudanarwa ta amfani da naurorin zamani.(Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GazaHamasKasar Sin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Taron Raya Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Kara Shaida Muhimmancin Zuba Jari A Kasar

Next Post

Ministan Wajen Angola: Manyan Ababen More Rayuwa Da Kamfanonin Sin Suka Gina A Kasar Angola Sun Inganta Ci Gaban Kasar

Related

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

7 hours ago
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata
Daga Birnin Sin

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

8 hours ago
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

10 hours ago
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya
Daga Birnin Sin

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

11 hours ago
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

18 hours ago
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

20 hours ago
Next Post
Ministan Wajen Angola: Manyan Ababen More Rayuwa Da Kamfanonin Sin Suka Gina A Kasar Angola Sun Inganta Ci Gaban Kasar

Ministan Wajen Angola: Manyan Ababen More Rayuwa Da Kamfanonin Sin Suka Gina A Kasar Angola Sun Inganta Ci Gaban Kasar

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.