Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian, ya ce Sin na adawa da duk wasu matakai da ka iya keta hurumin ‘yancin kai, da tsaro da mulkin yankunan kasar Iran. Kana tana tir da duk wani mataki na kara ta’azzara tashe-tashen hankula da zaman dar dar.
Lin, wanda ya bayyana hakan yayin taron manema labarai da ya gudana a Juma’ar nan, ya ce Sin na matukar mayar da hankali kan halin da ake ciki, tun bayan da Isra’ila ta kaddamar da hare-hare kan Iran, tana kuma matukar damuwa game da mummunan sakamakon da hakan ka iya haifarwa.
Ya ce, sake ta’azzarar yanayi a shiyyar ba zai yi wa kowa dadi ba, kuma Sin na kira ga daukacin sassan da lamarin ya shafa, da su aiwatar da matakan dawo da zaman lafiya da daidaito a shiyyar, tare da kaucewa kara rura wutar tashe-tashen hankula. Lin ya kuma ce Sin a shirye take, ta taka rawar gani wajen taimakawa, ta yadda za a sassauta halin da ake ciki. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp