ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Ta Ciri Tuta A Fannin Kimiyya Da Fasaha

by Sulaiman
1 month ago
Sin

A baya-bayan nan ne ministan ma’aikatar kimiyya da fasaha ta kasar Sin Yin Hejun da kwamishinan AU mai lura da harkokin ilimi, kimiyya da kirkire-kirkiren fasaha, Gaspard Banyankimbona, suka sanya hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna, a madadin gwamnatin jamhuriyar jama’ar kasar Sin da kungiyar AU, dangane da hadin gwiwar raya bangaren kimiyya da fasaha.

Karkashin wannan yarjejeniya, sassan biyu za su yi hadin kai wajen aiwatar da bincike, da gina dandalin hadin gwiwa na raya fasahohi, da aiwatar da musayar kwarewar fasahohi, da kirkire-kirkire da sana’o’i da sauransu.

Ina matukar taya nahiyar Afrika murna domin wannan abun farin ciki ne gare ta, ganin cewa idan batu ake na kimiyya da fasahar zamani, to dole ne a kira kasar Sin saboda dimbin ci gaban da ta samu da ma yadda take mayar da hankali wajen bincike da kirkire-kirkire da kuma yadda a kusan kullum, masana a kasar ke bullo da sabbin abubuwa na kimiyya da fasaha. Baya ga haka, babu mafi dacewa da ya kamata nahiyar Afrika ta hada gwiwa da ita a wannan fanni da ya wuce kasar Sin, duba da muradinta na ganin an ci gaba tare, an samu moriya tare da kuma yadda take taimakawa ba tare da rufa-rufa ko gindaya sharadi ko ma katsalandan cikin harkokin kasashe ba.

ADVERTISEMENT

Kasar Sin ta ciri tuta idan ana batu na kimiyya da fasaha. Cikin mizanin kirkire-kirkire na duniya da hukumar kula da hakkin mallaka ta duniya WIPO ta fitar a baya-bayan nan, a karon farko kasar Sin ta shiga jerin kasashe 10 dake kan gaba a fannin kirkire-kirkire, lamarin da ya tabbatar da ci gaban da kasar ke samu da kuma nuna kwalliya ta biyan kudin sabulu daga jajircewarta da manufofi da dimbin jarin da take zubawa bangaren.

Yayin da kasashe masu tasowa suka kasance koma baya, ci gaban kasar Sin zaburarwa ce a gare su cewa, su ma za su iya dogaro da karfinsu, kuma su samu ci gaba. Haka kuma, taimakonta gare su, ba shakka zai taka rawa wajen daga matsayinsu da kwarewarsu a fannin kimiyya da fasaha. Kamar yadda kullum nake fada, ci gaban kasar Sin, ci gaba ne ga kasashenmu na nahiyar Afrika domin duk wata nasara da ta samu, tana son su ma su samu. Don haka, ina ganin wannan hadin gwiwa da AU ta yi da Sin, dama ce ga kasashen Afrika ta kara karfinsu da kwarewa a bangaren ta yadda za su samu ci gaba kuma al’ummominsu su amfana.

LABARAI MASU NASABA

Kalubalantar Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Tamkar Wasa Da Wuta Ne

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kalubalantar Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Tamkar Wasa Da Wuta Ne
Daga Birnin Sin

Kalubalantar Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Tamkar Wasa Da Wuta Ne

November 14, 2025
Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 
Daga Birnin Sin

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

November 13, 2025
Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia
Daga Birnin Sin

Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

November 13, 2025
Next Post
Matatar Ɗangote Ta Zargi Ƙungiyar PENGASSAN Da Yi Wa Al’ummar Nijeriya Zagon Ƙasa

Matatar Ɗangote Ta Zargi Ƙungiyar PENGASSAN Da Yi Wa Al'ummar Nijeriya Zagon Ƙasa

LABARAI MASU NASABA

GORON JUMA’A

GORON JUMA’A

November 14, 2025
Kalubalantar Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Tamkar Wasa Da Wuta Ne

Kalubalantar Ka’idar “Kasar Sin Daya Tak A Duniya” Tamkar Wasa Da Wuta Ne

November 14, 2025
Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN

Musulmin da Aka Kashe  A Zamfara, Katsina Da Sokoto Sun Ninka Na Kiristoci A Tsakiyar Najeriya: MACBAN

November 14, 2025
Manzon Allah (SAW) A Matsayin Dan Gatan Allah 

Manzon Allah (SAW) A Matsayin Dan Gatan Allah 

November 14, 2025
Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma: Martani

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma: Martani

November 14, 2025
Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe

Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da DR Congo A Wasan Ƙarshe

November 14, 2025
Masana’antu Masu Zaman Kansu A Arewa Sun Yi Maraba Da Harajin Kashi 15 Na Shigo Da Man Fetur

Masana’antu Masu Zaman Kansu A Arewa Sun Yi Maraba Da Harajin Kashi 15 Na Shigo Da Man Fetur

November 14, 2025
Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati

Ronaldo Na Fuskantar Dakatarwar Wasanni Biyu Bayan Samun Jan Kati

November 14, 2025
Editoci Sun Yi Gargadi Kan Rushewar Kafofin Yada Labarai Sakamakon Matsin Tattalin Arziki

Editoci Sun Yi Gargadi Kan Rushewar Kafofin Yada Labarai Sakamakon Matsin Tattalin Arziki

November 14, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

Kotu Ta Yanke Wa Mutum 4 Hukuncin Kisa Kan Kashe Wani Makanike A Kano

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.