Kasar Sin ta kawo karshen aikin bayar da agajin gaggawa mafi girma a gundumar Rongjiang da ke lardin Guizhou, a yankin kudu maso yammacin kasar da misalin karfe 10 na safiyar ranar Lahadi, yayin da aka kammala ruwan saman da aka tafka kamar da bakin kwarya kamar yadda mahukuntan yankin suka bayyana.
Lardin Guizhou da wasu larduna masu iyaka da shi da ke kudu maso yammacin kasar Sin sun fuskanci mamakon ruwan sama tun daga ranar 18 ga watan Yuni, lamarin da ya haifar da mummunar ambaliyar ruwa, inda lamarin ya fi muni a yankin Rongjiang.
Mahukuntan yankin sun raba yankin zuwa kashi bakwai a matsayin wadanda ambaliyar ta fi shafa tare da kwashe mazauna zuwa wasu manyan wurare masu tudu. An kwashe fiye da mutane 40,000 zuwa wurare masu aminci tun karfe 6 na yammacin ranar Asabar saboda rigakafin hadarin ambaliyar.
Kasar Sin ta ware karin kudi yuan miliyan 100, kwatankwacin dalar Amurka miliyan 13.96 daga cikin kasafin kudin gwamnatin tsakiya don tallafa wa ayyukan ba da agajin gaggawa da farfado da lardin Guizhou da ambaliyar ruwan ta shafa, inda hakan ya kara adadin kudin da aka ware zuwa yuan miliyan 200, kamar yadda hukumar raya kasa da gudanar da gyare-gyare ta kasar ta bayyana. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp