A yau Alhamis, mahukuntan hukumar shige da fice ta kasar Sin sun sanar da cewa, kasar ta kara Indonesiya cikin shirinta na shiga kasar ba tare da biza ba na tsawon sa’o’i 240, wanda hakan ya kara yawan kasashen da suka cancanci shiga tsarin zuwa 55.
A cewar hukumar kula da shige da fice ta kasar, matafiya da suka cancanta da tsarin daga kasashe 55 da suka hada da Indonesiya, Rasha, da Ingila da sauransu na iya shiga kasar ta kowace daga cikin tashoshin jiragen ruwa guda 60 a cikin yankuna 24 na lardunan kasar kuma za su iya yada zango har na tsawon sa’o’i 240 ko kwanaki 10 ba tare da biza ba kafin su nufi wurin da suka dosa.
Manufar hakan wani bangare ne na kokarin da kasar Sin ke yi na bunkasa tafiye-tafiye da cudanya a tsakanin kasa da kasa. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp