• English
  • Business News
Thursday, September 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Ta Sha Alwashin Hada Hannu Da MDD Wajen Aiwatar Da Shawarar GGI 

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 hours ago
in Daga Birnin Sin
0
Sin Ta Sha Alwashin Hada Hannu Da MDD Wajen Aiwatar Da Shawarar GGI 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Firaministan kasar Sin Li Qiang, ya ce Sin a shirye take ta yi aiki da MDD, wajen aiwatar da shawarar nan ta tsarin shugabancin duniya ko GGI da Sin din ta gabatar, tare da dafawa wajen gina salon jagorancin duniya bisa adalci da daidaito tsakanin dukkanin sassa. 

 

Li Qiang, ya bayyana hakan ne a jiya Laraba, yayin ganawa da babban magatakardar MDD Antonio Guterres, a gefen babban taron mahawara na MDD karo na 80 dake gudana yanzu haka.

  • Collins Whitworth Zai Kafa Tarihin Shiga Kundin ‘Guinness World Record’ Tare Da Goyon Bayan Indomie
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Kakkaɓe Masu Amfani da Takardun Bogi a Ma’aikatunta

Li, ya ce cikin shekaru sama da 80 da suka gabata, MDD ta taka rawar gani da ba za a iya maye gurbinta ba a fannin wanzar da zaman lafiya da tsaro, da raya tattalin arziki da zamantakewar bil’adama, tare da kare hakkokin dan Adam.

 

Labarai Masu Nasaba

Sin Da Amurka Na Da Damar Cimma Karin Nasarori Tare Muddin Sun Nacewa Alkawuran Da Suke Dauka

Salon Zamanantarwa Irin Na Kasar Sin: Hanya Ce Mallakar Kasar Sin Wacce Kuma Ta Sada Duniya

Daga nan sai ya jaddada aniyar Sin, ta ci gaba da goyon bayan matsayi da ikon MDD, tare da mara baya ga sassan kasa da kasa wajen cimma nasarar amfani da dandalin MDDr a matsayin fagen karfafa shawarwari da hadin gwiwa, da tsare-tsare da aiwatar da matakai yadda ya kamata.

 

Haka kuma, a yayin zantawarsa da shugabar taron MDD karo 80 Annalena Baerbock, a gefen babban taron muhawarar majalissar dake gudana a halin yanzu, firaministan kasar Sin Li Qiang, ya ce Sin na goyon bayan gina MDD mai karin inganci da hangen nesa, ta hanyar gudanar da sauye-sauyen kyautata karko da nagartar ayyukanta. Ya kuma bayyana kakkarfan goyon bayan Sin ga ikon MDD, da rawar da take takawa a harkokin kasa da kasa.

 

Bugu da kari, a jiya Laraba, firaministan kasar Sin Li Qiang ya gana da shugabar hukumar gudanarwar kungiyar tarayyar Turai ta EU Ursula von der Leyen a birnin New York.

 

Yayin ganawar tasu Li Qiang ya ce, a bana ake cika shekaru 50 da kulla huldar diflomasiyya a tsakanin kasar Sin da kungiyar EU, kuma kasar Sin na fatan kungiyar EU za ta dauki matakai yadda ya kamata, da nufin inganta hadin gwiwa tsakanin bangarorin biyu don tallafa wa al’umma. Haka kuma, ya ce, kasar Sin na fatan kungiyar EU za ta cika alkawarinta na bude kasuwannin cinikayya da zuba jari, da kuma bin ka’idojin kungiyar cinikayya ta duniya wato WTO, da kaucewa shigar da siyasa da batun tsaron kasa cikin harkokin cinikayya.

 

Ya ce a matsayisu na manyan bangarori guda biyu a harkokin duniya, ya kamata kasar Sin da kungiyar EU, su sauke nauyin dake wuyansu, tare da ba da gudummawa a harkokin kasa da kasa, domin kare moriyarsu da ta gamayyar kasa da kasa.

 

A nata bangare, Ursula von der Leyen ta ce, kungiyar EU tana fatan aiwatar da ra’ayi daya da shugabannin bangarorin biyu suka cimma a yayin ganawarsu a bana, da kuma warware sabanin dake tsakaninsu ta hanyar yin shawarwari, ta yadda za a cimma sabbin sakamako a fannonin zuba jari, da kiyaye muhalli, da taimakawa kasashe masu tasowa da dai sauransu. Ta kuma kara da cewa, kungiyar EU ta yaba wa kasar Sin bisa himmarta a fannin fuskantar sauyin yanayi, tana kuma fatan zurfafa hadin gwiwa tsakanin bangarorin biyu a fannin, domin gaggauta aikin kwaskwarimar neman ci gaba ta hanyoyin kare muhalli, da tabbatar da dauwamammen ci gaban duniya.

 

A wannan rana kuma, firaministan kasar Sin Li Qiang ya gana da shugaban asusun Gates na kasar Amurka wato Bill Gates a birnin New York. Yayin da suke zantawa, Li Qiang ya ce cikin ’yan shekarun nan, kasar Sin ta samu gaggarumin ci gaba a fannin kiwon lafiya, ta kuma halarci hadin gwiwar raya kasashen duniya cikin himma da kwazo.

 

Ya ce kasar Sin tana fatan karfafa hulda tsakaninta da asusun Gates, domin habaka shirye-shiryen hadin gwiwa a fannin kiwon lafiya a duk fadin duniya, ta yadda za a tallafawa al’ummomin sassa daban daban, yayin da ake ba da gudummawar raya kasa da kasa. Haka kuma, ya ce, ya kamata kasashen Sin da Amurka su karfafa hadin gwiwar dake tsakaninsu, da kyautata tsarin gudanar da harkokin duniya, ta yadda za a tabbatar da bunkasuwar duniya cikin lumana.

 

A nasa bangare kuma, Bill Gates ya ce, dangantakar dake tsakanin kasar Sin da Amurka ita ce dangantaka mafiya muhimmanci a duniya, kuma asusun Gates da shi kansa, suna son ba da gudummawa ga aikin karfafa mu’amala tsakanin kasashen biyu, da kuma fuskantar kalubalolin duniya cikin hadin gwiwa. (Masu Fassara: Saminu Alhassan, Maryam Yang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Matashi Ya Kashe Kakanninsa Kan Abinci A Kano

Next Post

Sin Da Amurka Na Da Damar Cimma Karin Nasarori Tare Muddin Sun Nacewa Alkawuran Da Suke Dauka

Related

Sin Da Amurka Na Da Damar Cimma Karin Nasarori Tare Muddin Sun Nacewa Alkawuran Da Suke Dauka
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Na Da Damar Cimma Karin Nasarori Tare Muddin Sun Nacewa Alkawuran Da Suke Dauka

2 hours ago
Salon Zamanantarwa Irin Na Kasar Sin: Hanya Ce Mallakar Kasar Sin Wacce Kuma Ta Sada Duniya
Daga Birnin Sin

Salon Zamanantarwa Irin Na Kasar Sin: Hanya Ce Mallakar Kasar Sin Wacce Kuma Ta Sada Duniya

4 hours ago
An Yi Bikin Nune-Nunen Hotuna Da Bidiyo Na MDD Da Bikin Kade-Kaden Fina-Finai Masu Alaka Da Zaman Lafiya A Birnin New York
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Nune-Nunen Hotuna Da Bidiyo Na MDD Da Bikin Kade-Kaden Fina-Finai Masu Alaka Da Zaman Lafiya A Birnin New York

5 hours ago
Xi Ya Sanar Da Gudummawar Kasarsa Dangane Da Tunkarar Sauyin Yanayi Nan Zuwa 2035
Daga Birnin Sin

Xi Ya Sanar Da Gudummawar Kasarsa Dangane Da Tunkarar Sauyin Yanayi Nan Zuwa 2035

12 hours ago
Sin Ta Gudanar Da Bikin Cika Shekaru 70 Da Kafuwar Yankin Xinjiang Na Uygur Mai Cin Gashin Kai
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gudanar Da Bikin Cika Shekaru 70 Da Kafuwar Yankin Xinjiang Na Uygur Mai Cin Gashin Kai

13 hours ago
An Shirya Bikin Kaddamar Da Shirin Gaskiya Na Talabijin “Laszlo Hudec” Cikin Harshen Slovak A Kasar Slovakia
Daga Birnin Sin

An Shirya Bikin Kaddamar Da Shirin Gaskiya Na Talabijin “Laszlo Hudec” Cikin Harshen Slovak A Kasar Slovakia

23 hours ago
Next Post
Sin Da Amurka Na Da Damar Cimma Karin Nasarori Tare Muddin Sun Nacewa Alkawuran Da Suke Dauka

Sin Da Amurka Na Da Damar Cimma Karin Nasarori Tare Muddin Sun Nacewa Alkawuran Da Suke Dauka

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama ‘Yan Ta’adda 25, Sun Ceto Mutum 16 Da Aka Sace

Sojoji Sun Kama ‘Yan Ta’adda 25, Sun Ceto Mutum 16 Da Aka Sace

September 25, 2025
Sin Da Amurka Na Da Damar Cimma Karin Nasarori Tare Muddin Sun Nacewa Alkawuran Da Suke Dauka

Sin Da Amurka Na Da Damar Cimma Karin Nasarori Tare Muddin Sun Nacewa Alkawuran Da Suke Dauka

September 25, 2025
Sin Ta Sha Alwashin Hada Hannu Da MDD Wajen Aiwatar Da Shawarar GGI 

Sin Ta Sha Alwashin Hada Hannu Da MDD Wajen Aiwatar Da Shawarar GGI 

September 25, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

Matashi Ya Kashe Kakanninsa Kan Abinci A Kano

September 25, 2025
Salon Zamanantarwa Irin Na Kasar Sin: Hanya Ce Mallakar Kasar Sin Wacce Kuma Ta Sada Duniya

Salon Zamanantarwa Irin Na Kasar Sin: Hanya Ce Mallakar Kasar Sin Wacce Kuma Ta Sada Duniya

September 25, 2025
Saliba Ya Sabunta Kwantiraginsa Da Arsenal Har Tsawon Shekaru 5

Saliba Ya Sabunta Kwantiraginsa Da Arsenal Har Tsawon Shekaru 5

September 25, 2025
An Yi Bikin Nune-Nunen Hotuna Da Bidiyo Na MDD Da Bikin Kade-Kaden Fina-Finai Masu Alaka Da Zaman Lafiya A Birnin New York

An Yi Bikin Nune-Nunen Hotuna Da Bidiyo Na MDD Da Bikin Kade-Kaden Fina-Finai Masu Alaka Da Zaman Lafiya A Birnin New York

September 25, 2025
Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda

Gwamnatin Katsina Ta Bankaɗo Ma’aikatan Bogi 3,488

September 25, 2025
Labaran Xinjiang a Zane: Yadda Hamada Ta Zama Gonaki

Labaran Xinjiang a Zane: Yadda Hamada Ta Zama Gonaki

September 25, 2025
Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci

Tinubu Ya Nemi A Bai Wa Nijeriya Kujerar Dindindin A Kwamitin Tsaro Na Majalisar Ɗinkin Duniya 

September 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.