ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Collins Whitworth Zai Kafa Tarihin Shiga Kundin ‘Guinness World Record’ Tare Da Goyon Bayan Indomie

by Leadership Hausa
9 months ago
Indomie

A ranar 1 ga Oktoba, 2025, Collins Whitworth, ɗalibi a Jami’ar Bayero Kano (BUK), zai yi ƙoƙarin kafa tarihi a ƙoƙarinsa na karya karɓe kambun ‘Guinness’ na Duniya guda biyu a fannin fasahar zanen fuska: zanen fuska mai yawa cikin minti 3, da kuma fuska tarin yawa a cikin awa 1.

Yana ƙoƙarin karɓe kambun nasara daga Emilia Zakonnova da take riƙe da shi, wadda ta zana fuskar mutane 12 cikin minti 3, a ranar 30 ga Yuli, 2025. Wannan yunƙurin ba kawai nasarar Collins ba ce kaɗai, har ma ga ‘yan baiwa masu fasahar ƙirƙira a Nijeriya da matasa masu burin cimma burinsu na rayuwa.

  • An Kwace Kambun Hilda Baci A Gasar Dafa Abinci Ta Duniya
  • NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

Rayuwar Collins cike take da juriya da zuciyar jajircewa da ƙudure-ƙudure. Ko da yake ƙoƙarinsa na 2024 bai kai ga yin nasara ba, amma hakan ya ƙara masa ƙwazo da himma sosai, inda a yanzu ya dawo da ƙarfinsa. A cikin shekarar da ta gabata, ya sadaukar da awanni da yawa wajen ƙwarewa, daidaita sauri da yin tunani mai zurfi domin ya yi nasarar kafa tarihi.

ADVERTISEMENT

“Na koyi abubuwa da yawa daga yunƙurina na farko. A wannan karon na yi shirye-shirye na musanman tare da mayar da hankali da kuma ƙudurin yin nasara tare da goyon bayan Indomie, na yi imani za mu kafa tarihi tare,” in ji Collins.

Zanen fuska, ko da yake ana ganinsa a matsayin nishaɗi, fasaha ce mai ɗauke da ƙwarewa da take buƙatar ƙirƙira da kuzari ko saurin hannu. A wajen Collins, kowace fuska da ya zana tana bayyana wani saƙo tare da al’ada da kuma sanya farin ciki ga waɗanda suke sha’awar fasahar zane-zanensa. Yunƙurinsa na karɓe kambun tarihi na Kundin Guinness yana nuna yadda fasahar take da tasiri amma ba a bai wa ɓangaren dama sosai ba, yana haskaka yadda matasan Nijeriya su yi fice a duniya.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ake Wainar Masara Da Miyar Yaji

Yadda Ake Miyar Margi Da Kifin Tarwad

Indomie, a matsayin jigo da ta daɗe wajen nasarar samar da abinci mai gina jiki ga al’umma, tana alfahari da tallafawa wannan yunƙuri na kafa tarihi na Collins. Shekaru da dama, Indomie ta tallafa wa shirye-shiryen tallafawa a fannin ƙirƙira da ilimi da sana’o’i ga matasa. Tallafawa Collins, wata alamar nasara ce da take nuna ƙoƙarin Indomie na isar da saƙo mai ƙarfi ga jama’a wajen cimma manyan burika da muradan rayuwa da suke bukatar samun goyon baya da ƙarfafa guiwa.

Shigar cikin wannan al’amari wata babbar alama ce da take tabbatar da cewa wannan taron na tarihi ya sami haske da karramawa kamar yadda ya dace, taro ne da yake ƙarfafa wa matasan Nijeriya guiwa domin su samu nasarar cimma burinsu na rayuwa ta hanyar samun ƙwarin guiwa.

An tsara taron zai gudana a Kano a Ranar samun ‘yancin mulkin ƙasa Nijeriya, inda ake sa ran jama’a da iyalai da ɗalibai da masoya fasaha da ƙirƙira da ‘yan jarida daga ko’ina a cikin ƙasa za su hallarci taron. Masu kallo za su samu damar shaida tarihin da Collins zai kafa a lokaci wajen zana fuskar mutane sama da 12 a cikin minti 3 da kuma zana fuskar mutane fiye da 220 cikin awa 1.

Wannan taro da zai samu halartar jama’a zai bunƙasa al’ada da ƙirƙira kuma zai sa ranar ta kasance ta musanman ba kawai taro kadai ba, inda ranar za ta zama muhimmiyar ranar biki ta baje-kolin nuna baiwa da samar da haɗin kai.

Ƙoƙarin kafa wannan wannan tarihin da karbe kambun zai samu goyon baya da bai wa matasa dama ta musanman. Labarin Collins zai ja hankalin matasan Nijeriya waɗanda suke da mafarkin samun shahara a duniya. Kuma zai zama wata shaida ta cimma ƙuduri bayan samun dama da ƙarfafa guiwa daga Indomie a ɓangaren fasaha a Nijeriya.

A yayin da Kano ke shirin karɓar baƙi domin gudanar da wannan gagarumin biki a wannan rana mai ɗumbin tarihi, jama’a na cike da farin ciki a harabar jami’ar da kafafen sada zumunta da wurare daban-daban. Yunƙurin Collins ba kawai nasara ce ta ƙashin kansa ba; lokaci ne na tarihi wanda ke nuna ci gaban fasahar ƙirƙira a Nijeriya a idon duniya, kuma wata ‘yar manuniya ce da take nunawa kowa cewa samun manyan nasarori na farawa ne da sha’awa da ƙuduri da kuma samun tallafi.

Taken Indomie na “Mafarki mai yawa na haifar da nasarori masu yawa” an sanya shi a cikin muradin Collins. A ranar 1 ga Oktoba, duk idanu za su koma Kano domin ganin Collins Whitworth yadda zai kafa tarihi, ba kawai ta zanen fuska ba, har ma ta bayyana irin ƙwazonsa da baiwarsa da yadda zai zama abin alfahari ga ƙasa Nijeriya. Wannan taron wani muhimmin taro ne a duk faɗin Nijeriya a ɓangaren fasaha tare da ƙarfafa guiwar matasa wajen cikar muradan su.

Indomie
Leadership Hausa
+ postsBio
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    “Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”
  • Leadership Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/leadership-hausa/
    Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati Na Shekarar 2025, Dakta Zacch Adedeji

MASU ALAKA

Yadda Ake Wainar Masara Da Miyar Yaji
Girke-Girke

Yadda Ake Wainar Masara Da Miyar Yaji

June 14, 2026
Yadda Ake Miyar Margi Da Kifin Tarwad
Girke-Girke

Yadda Ake Miyar Margi Da Kifin Tarwad

June 6, 2026
Amfanin Man Kwakwa Guda 12
Girke-Girke

Amfanin Man Kwakwa Guda 11

May 17, 2026
Next Post
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje Da Gonaki A Kogi, Ta Tsaida Aiyuka A Legas

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje Da Gonaki A Kogi, Ta Tsaida Aiyuka A Legas

LABARAI MASU NASABA

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.