Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Guo Jiakun ya bayyana a yau Alhamis 6 ga watan nan cewa, Gaza ta Falasdinawa ce kuma tana daga wani bangare na halastattun yankunan Falasdinawa, don haka ba wuri ba ne da za a yi tayin siyasa da shi ba, ballan tana kuma a ce ta zama fagen wasan kura.
Ya bayyana haka ne a martanin da ma’aikatar ta mayar a kan kalaman da Shugaba Donald Trump na Amurka ya yi a kwanan nan cewa, yana so ya tare da karbe iko da ita.
Guo Jiakun ya bayyana cewa, kasar Sin tana goyon bayan halastaccen ikon al’ummar Falasdinu, sannan a ko da yaushe tana amanna da cewa, “Falasdinawa su mulki Falasdinu” wata muhimmiyar ka’ida ce da ta zama wajibi a yi aiki da ita wajen tafiyar da mulkin zirin Gaza bayan yaki, kuma tana adawa da yunkurin tilasta wa al’ummar Gaza yin gudun hijira da karfin tuwo. (Abdulrazaq Yahuza Jere)














