• English
  • Business News
Tuesday, September 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Daƙile Hare-haren ISWAP, Sun Bai Wa Magidanta 10,000 Kariya A Borno

by Sadiq
2 hours ago
in Manyan Labarai
0
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sojoji sun hana mayaƙan ISWAP kai hari a yankunan Banki da Bula Yobe, da ke Jihar Borno.

Waɗannan yankuna na magidanta sama da 10,000 da suka dawo gida bayan shekaru da dama suna gudun hijira saboda ta’addanci.

  • Nau’o’in Jirage Uku Sun Kammala Sauka Da Tashin Farko Bisa Taimakon Majaujawar Maganadisu A Jirgin Dako Na Fujian Na Kasar Sin
  • Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Bayyana Ra’ayin Kasar Kan Rikicin Falasdinu Da Isra’ila

Mayaƙan sun kai hari a ranar 18 ga watan Satumba, 2025, da nufin tilasta wa jama’a barin gidajensu.

Amma sojojin ƙasa tare da goyon bayan rundunar sojin sama ƙarƙashin Operation HADIN KAI sun yi nasarar fatattakar su.

Majiyoyin sojoji sun bayyana cewa dakarun da ke Banki da Bula Yobe, sun tsaya tsayin daka wajen kare mata, yara da tsofaffi.

Labarai Masu Nasaba

Majalisar Dattawa Ta Buɗe Ofishin Sanata Natasha

Majalisar Dokokin Ribas Za Ta Binciki Tsohon Kantoman Riƙo Ibok-Ete Ibas

Haka kuma sun tabbatar da cewa manoma da suka koma gonakinsu kwanan nan sun samu kariya.

Babu wanda aka sace ko ɗaya, yayin da jama’ar yankin ke ci gaba da zama lafiya.

A ranar 19 ga watan Satumba, Birigediya Janar Ugochukwu Unachukwu, wanda shi ne muƙaddashin kwamandan rundunar sojojin 7 Division, ya kai ziyara Banki don yaba wa sojoji kan jarumtar da suka nuna.

Ya ce ‘yan ta’addan sun yi mummunan rashi kuma ya tabbatar wa jama’a cewa rundunar sojojin Nijeriya za ta ci gaba da kare rayuka da dukiyoyi.

Sai dai rundunar ta tabbatar da cewa wani soja ya rasa ransa yayin kare mutanen, yayin da wasu suka ji rauni.

Sojojin sun ce wannan shaida ce ta jajircewar rundunar wajen tabbatar da zaman lafiya da kare ‘yan Nijeriya da suka koma gidajensu bayan gudun hijira.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BornoHariISWAPSojoji
ShareTweetSendShare
Previous Post

Majalisar Dattawa Ta Buɗe Ofishin Sanata Natasha

Next Post

Xi Jinping Zai Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 70 Da Kafuwar Yankin Xinjiang Na Uygur Mai Cin Gashin Kansa

Related

Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Buɗe Ofishin Sanata Natasha

3 hours ago
Kantoman Ribas Ya Naɗa Farfesa Lucky Worika A Matsayin Sakataren Gwamnati
Manyan Labarai

Majalisar Dokokin Ribas Za Ta Binciki Tsohon Kantoman Riƙo Ibok-Ete Ibas

4 hours ago
Rikicin Gonar Gado Ya Yi Ajalin Mutum Ɗaya, An Ƙone Gidaje A Filato
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Majalisar Dokokin Jihar Filato

5 hours ago
Yadda Aka Bai Wa Ousmane Dembélé Kyautar Ballon d’Or Ta 2025
Manyan Labarai

Yadda Aka Bai Wa Ousmane Dembélé Kyautar Ballon d’Or Ta 2025

9 hours ago
Jadawalin ‘Yan Wasa 30 Na Farko A Kyautar Ballon D’or Ta Bana
Manyan Labarai

Jadawalin ‘Yan Wasa 30 Na Farko A Kyautar Ballon D’or Ta Bana

18 hours ago
BUK
Manyan Labarai

Mataimakin Shugaban BUK Ya Buƙaci ‘Yan Siyasa Da Su Yi Koyi Da Tallafin Karatu Na Barau

23 hours ago
Next Post
Xi Jinping Zai Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 70 Da Kafuwar Yankin Xinjiang Na Uygur Mai Cin Gashin Kansa

Xi Jinping Zai Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 70 Da Kafuwar Yankin Xinjiang Na Uygur Mai Cin Gashin Kansa

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Zai Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 70 Da Kafuwar Yankin Xinjiang Na Uygur Mai Cin Gashin Kansa

Xi Jinping Zai Halarci Bikin Murnar Cika Shekaru 70 Da Kafuwar Yankin Xinjiang Na Uygur Mai Cin Gashin Kansa

September 23, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Sojoji Sun Daƙile Hare-haren ISWAP, Sun Bai Wa Magidanta 10,000 Kariya A Borno

September 23, 2025
Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja

Majalisar Dattawa Ta Buɗe Ofishin Sanata Natasha

September 23, 2025
Kantoman Ribas Ya Naɗa Farfesa Lucky Worika A Matsayin Sakataren Gwamnati

Majalisar Dokokin Ribas Za Ta Binciki Tsohon Kantoman Riƙo Ibok-Ete Ibas

September 23, 2025
Rikicin Gonar Gado Ya Yi Ajalin Mutum Ɗaya, An Ƙone Gidaje A Filato

‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Majalisar Dokokin Jihar Filato

September 23, 2025
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamnatin Kano Ta Tabbatar Da Ɓullar Cutar Mpox A Jihar

September 23, 2025
Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda

Katsina Za Ta Ɗauki Nauyin Karatun Mahaddata Alƙur’ani – Gwamna Radda

September 23, 2025
Yadda Aka Bai Wa Ousmane Dembélé Kyautar Ballon d’Or Ta 2025

Yadda Aka Bai Wa Ousmane Dembélé Kyautar Ballon d’Or Ta 2025

September 23, 2025
He Lifeng: Ya Kamata Sin Da Amurka Su Karfafa Dangantakar Tattalin Arziki Da Cinikayya Mai Dorewa Cikin Lumana

He Lifeng: Ya Kamata Sin Da Amurka Su Karfafa Dangantakar Tattalin Arziki Da Cinikayya Mai Dorewa Cikin Lumana

September 22, 2025
Sin Tana Maraba Da Kwararru Daga Bangarori Daban Daban Na Kasa Da Kasa Su Zo Kasar

Sin Tana Maraba Da Kwararru Daga Bangarori Daban Daban Na Kasa Da Kasa Su Zo Kasar

September 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.