Rundunar Sojojin Nijeriya sun yi nasarar kashe wasu manyan shugabannin ‘yan bindiga biyu da ake nema ruwa a jallo, Baldo da Baban Yara, tare da sauran yaransu.
Shugabannin sun kasance manyan tawagogi a yankin da ke musayar wadanda aka yi garkuwa da su a sansanonin jihohin Zamfara ko Katsina.
- Hanyoyi Goma Da Za Su Taimaka Wajen Gyaran Jiki
- Yawan Marasa Aikin Yi A Nijeriya Ya Karu Da Kaso 5 A Karshen 2023 – NBS
Wata majiyar leken asiri ta tsaro ta tabbatar wa PRNigeria cewa, an kashe ‘yan ta’addan ne a ranar Asabar a wani kazamin farmakin da sojoji suka kai a yankin Zamfara ko Katsina.
A cewar wata majiya mai tushe ta shaidawa PRNigeria cewa, an gudanar da harin cikin nasara domin babu wani dan ta’adda da ya tsira.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp