A ranar Litinin, 9 ga watan Yuni 2025, dakarun haɗin gwiwa na sojoji sun kai farmaki maɓoyar ƴan ta’adda na Boko Haram da ISWAP a Nzalgana da ke ƙaramar hukumar Gujba da kuma yankin Timbuktu Triangle.
Sanarwar da rundunar ta fitar a shafinta na X ta ce an kashe ƴan ta’adda da dama ciki har da jagororinsu.
- Mataimakin Firaministan Sin Ya Gana Da Ministar Kudin Birtaniya
- Shin Rashin Nasara Ya Rage Damar Yamal Na Ballon d’Or?
Daga cikin waɗanda aka kashe akwai Ameer Malam Jidda, wani babban kwamanda da ke da tasiri a ƙauyukan Ngorgore da Malumti.
Sojojin sun ƙara cewa sun kuma ƙwato makamai da wasu abubuwa masu muhimmanci a wani farmaki daban da suka kai Malamfatori.
A ‘yan kwanakin nan, hare-haren Boko Haram da ISWAP sun ƙaru, inda a watan da ya gabata ƙungiyar ta kai hari da jirgi mara matuƙi a garin Marte da ke Jihar Borno.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp