ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Ragargaji Haramtattun Matatun Mai 30 Da Cafke Mutum 42 Cikin Makonni 3 – DHQ

by Muhammad
2 years ago
Sojoji

Hedikwatar tsaro, (DHQ) ta ce dakarun hadin guiwa na Operations DELTA SAFE sun gano tare da lalata wuraren tace haramtacciyar matatar mai 30 tare da kama masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa su 42 a cikin makwanni uku.

Wannan na kunshe ne a cikin wata takarda da sashen yada labarai na dakarun tsaron ya fitar ta bakin, Birgediya Janar Abdullahi Ibrahim, kan ayyukan da sojoji suka yi a tsakanin 15 ga Yuni zuwa 6 ga Yuli 2023.

  • ‘Yansanda Sun Tabbatar Da Mutuwar Mutum 12 Yayin Tashin Bam A Wurin Hako Danyen Mai A Ribas
  • Matatar Man Dangote Za Ta Samar Da Karin Hasken Wutar Lantarki A Nijeriya – Gwamnan CBN

Ya ce sojojin a kokarinsu na tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a bangaren kula da harkokin kasuwanci a shiyyar Kudu maso Kudu na Nijeriya, sun gudanar da wani samame, kan yaki da haramtattun matatun man fetur a garuruwan Delta, Bayelsa, Ribas da Jihar Cross River.

ADVERTISEMENT

Ya ce an gudanar da samamen ne da nufin dakile masu aikata laifuka ‘yancin ci gaba da aika-aikar da suke.

Sakamakon haka, sojojin sun gano tare da lalata haramtattun matatun man fetur a wuraren hanya guda 30 da tankunan ajiyar mai 125, da jiragen ruwa na katako guda 21 da wasu ababe da dama.

LABARAI MASU NASABA

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

Sojojin sun kuma kwato litar danyen mai lita 1,675,700 da lita 74,500 na Man Fetur da Motoci 10 sai Babura 20 da Makamai 8 da alburusai iri-iri har 330 da cafke masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa su 42.

Ya ce, tuni an mika duk wasu kayayyakin da aka kwato daga hannun masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa da aka kama, an kuma mika su ga hukumar da ta dace domin daukar mataki.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

November 17, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

November 17, 2025
Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka
Manyan Labarai

Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

November 17, 2025
Next Post
Kwararren Burtaniya: Kasar Sin Ta Kama Hanyar Zama Jagaba A Duniya Cikin Kasashen Da Ba Sa Amfani Da Tsabar Kudi A Fannin Hada-Hada

Kwararren Burtaniya: Kasar Sin Ta Kama Hanyar Zama Jagaba A Duniya Cikin Kasashen Da Ba Sa Amfani Da Tsabar Kudi A Fannin Hada-Hada

LABARAI MASU NASABA

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

November 17, 2025
Hakimi, Osimhen Da Salah Ƴan Wasan Da Ke Takara A Ƙyautar Gwarzon Afrika

Hakimi, Osimhen Da Salah Ƴan Wasan Da Ke Takara A Ƙyautar Gwarzon Afrika

November 17, 2025
Tsohuwar Firaministan Bangaladesh Sheikha Hasina,

An Yanke Wa Tsohuwar Shugabar Bangladesh Hukuncin Kisa

November 17, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

November 17, 2025
Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

Mutane 42 Sun Mutu A Wani Hatsarin Tankar Dizal Da Motar Masu Umrah A Hanyar Makka

November 17, 2025
Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

Ba Mu Samu Labarin Kai Wa Laftanar Yerima Hari Ba – Ƴansanda

November 17, 2025
Sarki Sanusi Ya Shawarci Unguwannin Da Suka Fuskanci Matsalar Tsaro Su Sa Idon

Sarki Sanusi Ya Shawarci Unguwannin Da Suka Fuskanci Matsalar Tsaro Su Sa Idon

November 17, 2025
Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.