• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojojin Chadi Sun Fatattaki ‘Yan Boko Haram Zuwa Kamaru Da Nijar Da Nijeriya

by Rabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
7 months ago
in Labarai
0
Sojojin Chadi Sun Fatattaki ‘Yan Boko Haram Zuwa Kamaru Da Nijar Da Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin kasar Chadi ta fada cewa daruruwan mayakan Boko Haram na ficewa daga yankin tsakiyar Afirka suna tsallakawa zuwa kasashen Kamaru da Nijar da kuma Nijeriya.

 

Gidan talabijin din kasar ya rawaito mayakan sun tsere bayan arangama da sojojin Chadi a karshen mako, wanda ya yi sanadin kashe mayakan Boko Haram sama da 100 da kuma sojojin Chadi kusan 20.

  • Boko Haram Ta Hallaka Sojoji 40 A Chadi
  • MOFA: Kasar Sin Na Son Sanya Sabon Kuzari A Ci Gaban Tattalin Arzikin Yankin Asiya Da Tekun Fasifik Da Ma Duniya

Tashar talabijin ta kasar Chadi ta bayar da rahoton cewa, ana ci gaba da kai hare-hare kan sansanonin ‘yan Boko Haram, inda sojojin suka sami asarar rayukan kusan sojoji 20, tare da jikkata wasu 32 a wani artabu da suka yi da ‘yan ta’addar Boko Haram a yankin tafkin Chadi a ranar Asabar.

 

Labarai Masu Nasaba

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Sanarwar da gwamnatin kasar ta fitar ta ce kimanin mayakan Boko Haram 100 ne suka mutu, yayin da wasu 100 suka samu raunuka, inda mayakan na Boko Haram ke tserewa zuwa kasashen Kamaru da Nijeriya da kuma Nijar.

 

A farkon watan nan ne sojojin kasar Chadi suka kaddamar da wani farmaki da nufin fatattakar ‘yan ta’addar Boko Haram daga yankunan da ke kusa da tafkin Chadi, a cewar shugaban kasa, Janar Mahamat Idriss Deby.

 

Deby ya ce farmakin mai suna Haskanite, na zama a matsayin daukar fansar kashe sojojin gwamnati 40 a watan Oktoba, da kuma inganta tsaro ga fararen hula a yankin.

 

Hare-haren ya haifar da ‘da mai ido a makon da ya gabata, lokacin da Deby ya ce sojojin Kamaru da Nijeriya da kuma Nijar, wadanda dukkansu ke ba da gudummawar sojoji ga rundunar hadin gwiwa ta yaki da ta’addanci a yankin, sun yanke shawarar kin hada kai da harin na Chadi.

 

Kasashen Kamaru da Nijeriya da Nijar ba su bayar da wata sanarwa a bainar jama’a ba, da ke tabbatarwa ko musanta ikirarin na Deby ba, kuma Muryar Amurka ba ta iya tabbatarwa da kanta ba, ko kasashen uku sun zabi kin shiga aikin na Chadi.

 

Sojojin Kamaru sun ce tsaro ne kan iyakokin kasar da kuma kare fararen hula.

 

Deby ya ce ya shirya janye sojojinsa daga rundunar kasa da kasa da ke da kusan dakaru 11,000, saboda rashin samun abin da ya kira hadin kai tsakanin kasashe mambobin kungiyar na yaki da ta’addancin Boko Haram.

 

Chadi ba ta bayyana lokacin da za ta janye sojojinta daga rundunar hadin gwiwa da ke samun taimakon Majalisar Dinkin Duniya ba.

 

A shekara ta 2009 ne kungiyar Boko Haram ta kaddamar da tawaye da makamai ga gwamnatin Nijeriya, domin kafa Daular Musulunci. Tun daga lokacin yakin ya bazu zuwa kasashe makwabta kuma ya yi sanadiyar mutuwar mutane sama da 40,000 tare da raba sama da miliyan 3 da muhallansu a cewar Majalisar Dinkin Duniya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Zai Tafi Brazil Kwana Biyar Bayan Dawo Wa Daga Saudiya

Next Post

CMG Da El Comercio Group Na Kasar Peru Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Zurfafa Hadin Gwiwa

Related

Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

23 minutes ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

3 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

6 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

7 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

16 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

18 hours ago
Next Post
CMG Da El Comercio Group Na Kasar Peru Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Zurfafa Hadin Gwiwa

CMG Da El Comercio Group Na Kasar Peru Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Zurfafa Hadin Gwiwa

LABARAI MASU NASABA

Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.