• English
  • Business News
Friday, October 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojojin Nijeriya Sun Dauki Alhakin Kai Harin Bam Cikin Kuskure A Wurin Taron Mauludi A Kaduna

by Sulaiman
2 years ago
Sojojin Nijeriya

Gwamnatin jihar Kaduna ta ce, sojojin Nijeriya sun dauki alhakin jefa bam a Tudun Biri da ke karamar hukumar Igabi a jihar Kaduna wanda ya yi sanadin mutuwar mutane akalla 30 a ranar Lahadi.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa, an kashe mutane da dama a kauyen Tudun Biri da ke karamar hukumar Igabi a jihar Kaduna bayan da wani jirgin soji ya jefa bam a yayin da ake gudanar da taron Mauludi.

  • Ranar Nakasassu: Gwamna Uba Sani Ya Nanata Kudirin Shigar Da Su Harkokin Jihar Kaduna
  • Yadda Matakin Raya Kauyuka Da Sin Ta Dauka Ke Taimakawa Kawar Da Talauci Da Ma Yayata Aladun Kasar

Tun da farko dai, rundunar sojin saman Nijeriya, NAF ta musanta alhakin kai harin.

A cewar sanarwar da Daraktan hulda da jama’a da yada labarai na rundunar sojin saman Nijeriya, Commodore Edward Gabkwet ya fitar, “NAF ba ta kai wani hari a Kaduna cikin sa’o’i 24 da suka gabata ba.”

Sai dai, kwamishinan tsaro na cikin gida da harkokin cikin gida Samuel Aruwan, ya ce babban hafsan rundunar soji ta 1 ta Nijeriya da kwamandan rundunar Operation Whirl Punch, Manjo Janar VU Okoro, sun amince cewa, lamarin ya faru ne cikin kuskure yayin da rundunar sojojin Nijeriya ke ci gaba da yaki da ‘yan ta’adda a yayin gudanar da ayyukan rundunar na kullum.

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai kula da harkokin tsaron cikin gida ya raba wa manema labarai jim kadan bayan da mataimakiyar gwamnan, Dakta Hadiza Balarabe ta gana da malaman addinin musulunci, da sarakunan gargajiya, da shugabannin hukumomin tsaro.

An gudanar da taron ne a gidan gwamnati na Sir Kashim Ibrahim, Kaduna a ranar Litinin.

Ya kara da cewa, har yanzu ana ci gaba da gudanar da aikin ceto tare da kwashe dimbin wadanda suka jikkata zuwa asibitin koyarwa na Barau Dikko.

Sanarwar ta kara da cewa, mataimakiyar gwamnan ta jajantawa iyalan wadanda abin ya shafa yayin da ta yi addu’ar Allah ya jikan wadanda suka rasu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

October 10, 2025
Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi
Manyan Labarai

Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Karyata Batun Yi Wa Kiristoci Kisan Ƙare Dangi

October 10, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 
Manyan Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Zaɓi Farfesa Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC 

October 9, 2025
Next Post
Babban Edita Dan Kasar Ghana: A Bayyana Yadda Sin Da Afirka Suke Hadin Gwiwa Da Juna

Babban Edita Dan Kasar Ghana: A Bayyana Yadda Sin Da Afirka Suke Hadin Gwiwa Da Juna

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

Xi Ya Taya Kim Jong Un Murnar Cikar Jam’iyyar WPK Shekaru 80 Da Kafuwa

October 10, 2025
An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 

An Zuba Jarin Dala Biliyan 5.2, An Sa Hannu Kan Yarjejeniyoyi 47 A Taron Tattalin Arziƙin Bauchi 

October 10, 2025
Nijeriya

Haramcin Haƙar Ma’adanai: Majalisa Za Ta Kawo Ƙarshen Asarar Dala Biliyan 9 Duk Shekara

October 10, 2025
Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

Ƴansanda Sun Ceto Mutane Uku Da Aka Sace A Kano

October 10, 2025
Yadda Rashin Isassun Malaman Turanci Da Lissafi Ke Shafar Ingancin Ilimi A Nijeriya (3)

Yadda Za A Magance Yawaitar Malaman Da Ba Su Cancanta Ba A Nijeriya – TRCN

October 10, 2025
Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

Gwamnatin Katsina Ta Rufe Makarantu 32 Masu Zaman Kansu Da Ba Su Da Lasisi

October 10, 2025
Sojojin Nijeriya

Burin ‘Yan Nijeriya Bai Cika Ba Tun Bayan Samun ‘Yancin Kai

October 10, 2025
Matatar dangote

ACF Ta Yi Zargin Shiri Na Musamman Don Rusa Matatar Man Dangote

October 10, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

October 10, 2025
Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

Gwamnatin Kogi Ta Yaba Wa Tinubu Kan Naɗin Amupitan Shugaban INEC

October 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.