ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojojin Nijeriya Sun Dauki Alhakin Kai Harin Bam Cikin Kuskure A Wurin Taron Mauludi A Kaduna

by Sulaiman
3 years ago
Sojojin Nijeriya

Gwamnatin jihar Kaduna ta ce, sojojin Nijeriya sun dauki alhakin jefa bam a Tudun Biri da ke karamar hukumar Igabi a jihar Kaduna wanda ya yi sanadin mutuwar mutane akalla 30 a ranar Lahadi.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa, an kashe mutane da dama a kauyen Tudun Biri da ke karamar hukumar Igabi a jihar Kaduna bayan da wani jirgin soji ya jefa bam a yayin da ake gudanar da taron Mauludi.

  • Ranar Nakasassu: Gwamna Uba Sani Ya Nanata Kudirin Shigar Da Su Harkokin Jihar Kaduna
  • Yadda Matakin Raya Kauyuka Da Sin Ta Dauka Ke Taimakawa Kawar Da Talauci Da Ma Yayata Aladun Kasar

Tun da farko dai, rundunar sojin saman Nijeriya, NAF ta musanta alhakin kai harin.

ADVERTISEMENT

A cewar sanarwar da Daraktan hulda da jama’a da yada labarai na rundunar sojin saman Nijeriya, Commodore Edward Gabkwet ya fitar, “NAF ba ta kai wani hari a Kaduna cikin sa’o’i 24 da suka gabata ba.”

Sai dai, kwamishinan tsaro na cikin gida da harkokin cikin gida Samuel Aruwan, ya ce babban hafsan rundunar soji ta 1 ta Nijeriya da kwamandan rundunar Operation Whirl Punch, Manjo Janar VU Okoro, sun amince cewa, lamarin ya faru ne cikin kuskure yayin da rundunar sojojin Nijeriya ke ci gaba da yaki da ‘yan ta’adda a yayin gudanar da ayyukan rundunar na kullum.

LABARAI MASU NASABA

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Dakatar Da INEC Game Da Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu

Tinubu Ya Kaddamar Da Katafaren Gidajen Alƙalan Kotun Ɗaukaka Ƙara A Abuja

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai kula da harkokin tsaron cikin gida ya raba wa manema labarai jim kadan bayan da mataimakiyar gwamnan, Dakta Hadiza Balarabe ta gana da malaman addinin musulunci, da sarakunan gargajiya, da shugabannin hukumomin tsaro.

An gudanar da taron ne a gidan gwamnati na Sir Kashim Ibrahim, Kaduna a ranar Litinin.

Ya kara da cewa, har yanzu ana ci gaba da gudanar da aikin ceto tare da kwashe dimbin wadanda suka jikkata zuwa asibitin koyarwa na Barau Dikko.

Sanarwar ta kara da cewa, mataimakiyar gwamnan ta jajantawa iyalan wadanda abin ya shafa yayin da ta yi addu’ar Allah ya jikan wadanda suka rasu.

Sojojin Nijeriya
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    An Kaddamar Da Wani Kwas Na Horar Da Kwararru Kan Killace Kananan Makamai Na Sin Da MDD Da Afirka 
  • Sulaiman
    Mataimakin Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Shugabanni Game Da Barkewar Cutar Ebola
  • Sulaiman
    Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Dakatar Da INEC Game Da Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu
  • Sulaiman
    Tattalin Arzikin Sin Ya Tafiya Cikin Kwanciyar Hankali

MASU ALAKA

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Dakatar Da INEC Game Da Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu
Manyan Labarai

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Dakatar Da INEC Game Da Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu

June 16, 2026
Tinubu Ya Kaddamar Da Katafaren Gidajen Alƙalan Kotun Ɗaukaka Ƙara A Abuja
Manyan Labarai

Tinubu Ya Kaddamar Da Katafaren Gidajen Alƙalan Kotun Ɗaukaka Ƙara A Abuja

June 16, 2026
Sabbin Ministoci
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Kira Zaman Gaggawa A Ranar 23 Ga Yuni Kan Matsalar Tsaro

June 16, 2026
Next Post
Babban Edita Dan Kasar Ghana: A Bayyana Yadda Sin Da Afirka Suke Hadin Gwiwa Da Juna

Babban Edita Dan Kasar Ghana: A Bayyana Yadda Sin Da Afirka Suke Hadin Gwiwa Da Juna

LABARAI MASU NASABA

An Kaddamar Da Wani Kwas Na Horar Da Kwararru Kan Killace Kananan Makamai Na Sin Da MDD Da Afirka 

An Kaddamar Da Wani Kwas Na Horar Da Kwararru Kan Killace Kananan Makamai Na Sin Da MDD Da Afirka 

June 16, 2026
Mataimakin Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Shugabanni Game Da Barkewar Cutar Ebola

Mataimakin Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Shugabanni Game Da Barkewar Cutar Ebola

June 16, 2026
Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Dakatar Da INEC Game Da Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Dakatar Da INEC Game Da Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu

June 16, 2026
Tattalin Arzikin Sin Ya Tafiya Cikin Kwanciyar Hankali

Tattalin Arzikin Sin Ya Tafiya Cikin Kwanciyar Hankali

June 16, 2026
Gaza

Farashin Mai Ya Faɗi Ƙasa Da Dala 80 Bayan cimma Yarjejeniyar Amurka Da Iran

June 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Myanmar

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Myanmar

June 16, 2026
Tinubu Ya Kaddamar Da Katafaren Gidajen Alƙalan Kotun Ɗaukaka Ƙara A Abuja

Tinubu Ya Kaddamar Da Katafaren Gidajen Alƙalan Kotun Ɗaukaka Ƙara A Abuja

June 16, 2026
Kasar Sin Na Samar Da Managarcin Yanayi Na Bunkasa Kirkire-kirkire Ga Masana’antun Kasa Da Kasa

Kasar Sin Na Samar Da Managarcin Yanayi Na Bunkasa Kirkire-kirkire Ga Masana’antun Kasa Da Kasa

June 16, 2026
Kogi: Mambobin APC Sun Koma PDP, Sun Mara Wa Natasha Baya Domin Wa’adi Na Biyu

Kogi: Mambobin APC Sun Koma PDP, Sun Mara Wa Natasha Baya Domin Wa’adi Na Biyu

June 16, 2026
Sin Na Goyon Bayan Ci Gaban Manyan Kamfanonin Kasa Da Kasa

Sin Na Goyon Bayan Ci Gaban Manyan Kamfanonin Kasa Da Kasa

June 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.