• English
  • Business News
Tuesday, June 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

by Mairo Muhammad Mudi
2 days ago
in Bakon Marubuci
0
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin shirin kidayar jama’a ta shekarar 2006, Tsohon Shugaban Hukumar Kidayar Jama’a ta Kasa, Cif Samuila Danko Makama, ya gudanar da aikin wayar da kai a Suleja. A cikin jawabin nasa, ya bayyana yadda kimar yawan jama’ar garin yake na musamman, saboda kusancinsa da Babban Birnin Tarayya. A martaninsa ga wannan jawabi, Sarkin Suleja, Malam Muhammadu Awwal Ibrahim, ya ce; “Duk sanda Abuja ta yi tari, Suleja sai ta kamu da mura.”

Mai Martaba ya fadi gaskiya, domin a lokacin, an fara rusa gine-ginen da ba bisa ka’ida ba a Gwagwa, Karmo, Jiwa da kewaye, kuma yawancin wadanda abin ya shafa, sun kwarara zuwa Suleja. Duk da haka, babu wani taimako na musamman da aka bai wa garin domin daukar wannan nauyi. Wannan ya kai ga wata cikakkiyar wallafa a jaridar Daily Trust a ranar 31 ga Oktoba, 2006, wanda Malam Nasiru Imam ya rubuta, mai taken: ‘Abuja Grows, Suleja Groans’.

  • Wakilin Sin Ya Soki Yadda Amurka Ke Tafiyar Da Kudurin Takunkuman Sudan Ta Kudu
  • Zulum Ya Ba Da Tallafin Karatu Ga Mata ‘Yan Asalin Jihar Da Suka Samu Maki 250 A JAMB

Taken binciken rubutun digirina na biyu a Jami’ar Ahmadu Bello, Zaria (ABU), ya kasance: Tasirin Abuja ga ci gaban Suleja. Daga binciken da na yi a Ma’aikatar Kudi ta Jihar Neja, na gano cewa; a shekarar 1994, fiye da shekara 30 da suka wuce, jimillar kudin da jihar ta samu daga hanyoyin ciki, bai wuce Naira miliyan 64 ba. Sai dai, Suleja kadai ta bayar da Naira miliyan 24, wanda ya kai kashi 37.8 cikin 100. A wancan lokaci, albashina a matsayin ma’aikaci a matakin Lebel 09 a Hukumar FCDA, bai kai Naira 1,000 ba.

Ka’idar biyan haraji ita ce, domin samar da ababen more rayuwa da ayyuka ga al’umma. Amma dukkanin ma’aikatan Abuja da iyalansu da ke zaune a Suleja, suna amfana da asibitoci, makarantun gwamnati da sauran ayyuka da ke garin Suleja. Sai dai harajinsu, wanda ma’aikatansu ke cirewa daga albashi, ba a mayar da shi ga gwamnatin da ke samar da wadannan ayyuka a Suleja ba.

Mutanen Suleja, sun jima suna kira da a dawo da harajin PAYE na ma’aikatan Abuja da ke zaune a Suleja, saboda suna da yakinin cewa; hakan zai sa Gwamnatin Jihar Neja ta fi kula da Suleja. An amince da hakan, sannan kuma yanzu ana karbarsa a boye-boye, amma babu wani canji da aka gani a kasa.

Labarai Masu Nasaba

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (2)

Ta Ya Ake Gudanar Da Nagartacciyar Rayuwa?

Yanzu haka, akalla ana iya karbar sama da Naira miliyan 100 daga wannan PAYE a kowane wata. Wasu hanyoyin samun kudaden shiga, sun hada da haya na kasa (ground rent), harajin haya (tenement rate), da harajin wuraren kasuwanci. Har ma da noma, ana sa wa haraji a Suleja, duk da cewa; gwamnan jihar manomi ne. Ya dace gwamnati ta tabbatar da cewa; ana samar da kayayyakin more rayuwa masu inganci a Suleja, ko da don a samu karin haraji ne.

Idan har gwamnatin tarayya ba ta yaba da sadaukarwar da Suleja ta yi ba, to akalla Gwamnatin Jihar Neja; ya kamata ta fi mayar da hankali wajen samar da ci gaba a Suleja, domin karrama gudunmawar da garin ke bayarwa wajen samun kudaden shiga ga jihar. Har ila yau, adalci ne a dawo da abin da aka karba ta hanyar ayyuka ga al’umma.

Tsohon Gwamna, Babangida Aliyu ya ce; gwamnatinsa ta gina titin cikin gari na kilomita 10 a kowace karamar hukuma. Amma ba a kai wa Suleja kilomita uku ba. Titin Gwazunu da aka ce an gyara, bai kai shekara biyu ba ya lalace. Aliyu kuma ya zo da burin aikin Twin City, ciki har da aikin titin Madalla mai layi biyu, a cikin bashi da aka fito da shi. Amma aikin da bashin duk sun bace bat kamar iska.

Gwamnatin yanzu ta sanar da shirin samar da tituna na tsawon kilomita 50 a kowanne daga cikin garuruwa uku: Bida, Kontagora da kuma Suleja. An kaddamar da aikin a sauran wuraren amma ban da Suleja ba.

Watakila aikin titin da aka fara shi ne, wanda ake gina magudanan ruwa marasa inganci a gefen titin Maje zuwa Madalla da kuma hanyar Kaduna. Wannan abin takaici ne. Abu mafi muni shi ne, tsoffin magudanan ruwa da Gwamna Kure ya gina fiye da shekaru 20 da suka wuce, wadanda yanzu ake maye gurbinsu, sun fi wadanda ake ginawa yanzu inganci.

Titin Maje zuwa Madalla na daga cikin manyan titunan tarayya, ‘Trunk A-124’. Ma’ana, gwamnatin jiha, na sa ran gwamnatin tarayya za ta biya su bayan shekara 10. Amma ta yaya aiki marar inganci irin haka zai cancanci a biya kudinsa? Idan har gwamnatin yanzu ta ki gyarawa, ta ci gaba da biyan kwangilar wanda ko sunansa ba a so a sani, duk da gurbataccen aikin da korafi masu yawa, hakan yana nuna cewa; abin da ta fi mayar da hankali a kai shi ne kudi, ba aiki ko jin dadin jama’a ba. haka zalika kuma, wannan gwamnatin ba ta damu da matsalolin da za su bar wa gwamnati mai zuwa ba.

Masu gidaje, yawancinsu ‘yan asalin garin wadanda aikin ke shirin shafar su ne, don haka dole ne a biya su diyya tare da sake musu matsugunai. Amma har yanzu, babu wani shiri na sake matsugunan ko kididdigar diyya da aka sanar a Suleja. Amma an gudanar da hakan a wasu al’ummomi a cikin jihar.

Babu shakka, ikon gwamnati ya shafi dukkanin Jihar Neja, ba Suleja kadai ba. Amma Hassan da Hussaini duka suna da hakkin da ya caccanta a ba su. Sai dai, ba dai-dai ba ne a tauye hakkin Hassan don a amfanar da Hussaini. A bayyane yake karara, inda ake samun kudin shiga a Jihar Neja, ba can ake yi da su ba. A gaggauta gyara tunda lokaci bai kure ba.

Alhamdulillah!


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Suleja
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22

Next Post

NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

Related

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (2)
Bakon Marubuci

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (2)

2 weeks ago
Ta Ya Ake Gudanar Da Nagartacciyar Rayuwa?
Bakon Marubuci

Ta Ya Ake Gudanar Da Nagartacciyar Rayuwa?

2 months ago
Waraka Daga Bashin Ketare
Bakon Marubuci

Waraka Daga Bashin Ketare

2 months ago
Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai
Addini

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [21]

2 months ago
Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai
Addini

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [20]

2 months ago
Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai
Addini

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [19]

2 months ago
Next Post
NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

NDLEA Ta Cafke Masu Tura Alhazai Saudiyya Domin Safarar Hodar Iblis Zuwa Kasar

LABARAI MASU NASABA

An Yi Balaguro Miliyan 657 A Tsakanin Yankunan Kasar Sin Lokacin Bikin Duanwu Na Bana

An Yi Balaguro Miliyan 657 A Tsakanin Yankunan Kasar Sin Lokacin Bikin Duanwu Na Bana

June 2, 2025
NAF Ta Kashe ‘Yan Bindiga Da Dama A Zamfara

Jiragen Yakin NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 20, ‘Yan Banga 2 A Zamfara

June 2, 2025
Ministan Tsaron Singapore: Sinawa Ne Za Su Iya Tantance Batun Taiwan

Ministan Tsaron Singapore: Sinawa Ne Za Su Iya Tantance Batun Taiwan

June 2, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranakun Hutu Domin Bukukuwan Sallah

June 2, 2025
Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

Hadin Gwiwa Hanya Ce Madaidaiciya Wajen Kiyaye Tsaron Shiyya

June 2, 2025
Malaman Jami’ar Gombe Sun Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba-ta-gani 

Tsaro: ‘Yansanda Sun Kulle Tashar Dadin Kowa Da Sauransu A Gombe 

June 2, 2025
Mataimakin shugaban kasa

Shettima: Shekaru Biyu Na Mataimaki, Jagora Mai Hangen Nesa Da Kawo Sauyi Nagari

June 2, 2025

Alƙalai Da Lauyoyi Sun Yi Cirko A Gaban Kotu Bayan Fara Yajin Aikin Ma’aikatan Shari’a

June 2, 2025
Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

June 2, 2025
Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

Za A Samu Mamakon Ruwan Sama Da Hazo Daga Litinin Zuwa Laraba A Nijeriya

June 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.