• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina: Nasara Ko Matsala?

byEl-Zaharadeen Umar
2 weeks ago
Sulhu

Zuwa yanzu kananan hukumomi goma sha daya daga cikin 18 da suke fama da matsanancin rashin tsaro sakamakon hare-haren ‘yan bindiga da aka shafe shekara da shekaru ana yi suka kulla yarjejeniyar zaman sulhu da barayin daji.

Kananan hukumomin sun hada da Jibia da Batsari da Safana da Danmusa da Kurfi da Musawa da Matazu da Faskari da Kankara da Sabuwa da kuma Dandume inda yanzu ake sa ran Dutsinma zata bi sahu.

  • Sojoji Sun Kama ‘Yan Ta’adda 25, Sun Ceto Mutum 16 Da Aka Sace
  • Saliba Ya Sabunta Kwantiraginsa Da Arsenal Har Tsawon Shekaru 5

Sulhu da barayin daji da ake cigaba da aiwatarwa a jihar Katsina Na cigaba da haifar da muhawara a tsakanin masana da kuma sauran al’umma.

Maganganun da ke fitowa daga al’ummar da wannan matsala ta shafa shi ne, su wannan sulhu ya zama alheri gare su, kuma suna fatan cewa hakan za ta dore.

A gefe guda kuma masana na cewa idan har za a yi sulhu da barayin daji kuma a kyalesu da makamai, to akwai sake wai an dafa kaza an ba mai ita kai…

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

Wanda duk zai gaya maka gaskiya musamman wanda yake zaune ko ya ke zuwa wuraren da aka samu matsalar tsaro a wasu kananan hukumomi na jihar Katsina zai fada maka cewar an samu zaman lafiya fiye da lokutan baya.

An sha ruwaito wadanda wannan bala’i ya shafa suna maida martani ga masu suka sulhu da cewa duk wanda baya goyon bayan wannan sulhu dan ba a wannan yanki yake da zama ba.

Sai dai kuma yin sulhu da barayin daji ba yana nufin an samu zaman lafiya dari-bisa-dari ba. Ana dai samun saukin kai hare-haren ‘yan bindigar amma ba wai an daina ba ne baki daya.

To, ta ya ya al’umma za su amfana da wannan yarjejeniyar zaman sulhu da barayin daji, ana iya cewa hakan zai taimaka ta wajen huldar kasuwancin kiwo da kuma noma da ya fara zama tarihi a wasu wurare da ake wannan ta’addanci.

Idan aka duba salon da barayin daji suke amfani da shi bayan kaddamar da yarjejeniyar zaman sulhu shi ne, duk karamar hukumar da aka wannan sulhu to za su rage kai hare-hare Sannan za su sako wadanda suke tsare da su.

Haka kuma su kan kai hari ne a sauran kananan hukumomin da ba a kulla wannan yarjejeniya ta zaman lafiya da su ba, su yi barna su yi kisa su kwashe kayayyakin da jama’a.

Irin haka na ci gaba da faruwa, misali an yi zaman sulhu da barayin daji a karamar hukumar Kankara amma a satin da ya gabata rahotanni sun bayyana cewa an je an sace mutum 60 a garin Zango da Kankara.

Haka abin yake a karamar hukumar Faskari inda suka je garin Tafoki suka kwashe mashinan jama’a a ya yin da suke cikin gona suna aiki.

Sannan abubuwan da suka bayyana shine ana cigaba da kai hare-hare jefi-jefi kuma ana cigaba da satar jama’a da neman kudin fansa tare da sauran abubuwa marasa dad’i.

A bangaren barayin daji kuwa tuni harkoki suka fara kankama inda yanzu haka suke shigowa gari cin kasuwa da zuwa asibiti domin neman lafiyar su da ta iyalan su.

Ita ma gwamnatin jihar Katsina ta bada tabbacin cewa zata tallafawa wadanda wannan iftila’i ya shafa da jari da makarantu da asibitoci da sauran kayayyakin more rayuwa.

Gwamna Malam Dikko Umar Radda ya jaddada cewa hatta ‘yan bindigar da suka rungumi zaman lafiya za a taimaka masu da jari domin yin sana’a da za su dogara da kan su.

Gwamnan dai ya sha soka akan yadda rana tsaka ya yi mi’ara koma baya akan matsayar da ta cewa ba zai taba yin sulhu da barayin daji ba, sai dai idan ‘yan bindigar suka sha wuta suka mika kai.

Haka kuma daya daga hadiman gwamna Radda Jamilu Isma’il Mabai ya bayyana cewa ‘yan bindiga ne da kan su suka sha wuta daga jami’an tsaro suka nemi ayi sulhun ba gwamnati ba ce.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Labarai

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya
Labarai

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Next Post
A Karo Na Hudu ’Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Yi Nasarar Kammala Ayyukansu A Wajen Kumbon

A Karo Na Hudu ’Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Yi Nasarar Kammala Ayyukansu A Wajen Kumbon

LABARAI MASU NASABA

An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version