ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina: Nasara Ko Matsala?

by El-Zaharadeen Umar
10 months ago
Sulhu

Zuwa yanzu kananan hukumomi goma sha daya daga cikin 18 da suke fama da matsanancin rashin tsaro sakamakon hare-haren ‘yan bindiga da aka shafe shekara da shekaru ana yi suka kulla yarjejeniyar zaman sulhu da barayin daji.

Kananan hukumomin sun hada da Jibia da Batsari da Safana da Danmusa da Kurfi da Musawa da Matazu da Faskari da Kankara da Sabuwa da kuma Dandume inda yanzu ake sa ran Dutsinma zata bi sahu.

  • Sojoji Sun Kama ‘Yan Ta’adda 25, Sun Ceto Mutum 16 Da Aka Sace
  • Saliba Ya Sabunta Kwantiraginsa Da Arsenal Har Tsawon Shekaru 5

Sulhu da barayin daji da ake cigaba da aiwatarwa a jihar Katsina Na cigaba da haifar da muhawara a tsakanin masana da kuma sauran al’umma.

ADVERTISEMENT

Maganganun da ke fitowa daga al’ummar da wannan matsala ta shafa shi ne, su wannan sulhu ya zama alheri gare su, kuma suna fatan cewa hakan za ta dore.

A gefe guda kuma masana na cewa idan har za a yi sulhu da barayin daji kuma a kyalesu da makamai, to akwai sake wai an dafa kaza an ba mai ita kai…

LABARAI MASU NASABA

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

Wanda duk zai gaya maka gaskiya musamman wanda yake zaune ko ya ke zuwa wuraren da aka samu matsalar tsaro a wasu kananan hukumomi na jihar Katsina zai fada maka cewar an samu zaman lafiya fiye da lokutan baya.

An sha ruwaito wadanda wannan bala’i ya shafa suna maida martani ga masu suka sulhu da cewa duk wanda baya goyon bayan wannan sulhu dan ba a wannan yanki yake da zama ba.

Sai dai kuma yin sulhu da barayin daji ba yana nufin an samu zaman lafiya dari-bisa-dari ba. Ana dai samun saukin kai hare-haren ‘yan bindigar amma ba wai an daina ba ne baki daya.

To, ta ya ya al’umma za su amfana da wannan yarjejeniyar zaman sulhu da barayin daji, ana iya cewa hakan zai taimaka ta wajen huldar kasuwancin kiwo da kuma noma da ya fara zama tarihi a wasu wurare da ake wannan ta’addanci.

Idan aka duba salon da barayin daji suke amfani da shi bayan kaddamar da yarjejeniyar zaman sulhu shi ne, duk karamar hukumar da aka wannan sulhu to za su rage kai hare-hare Sannan za su sako wadanda suke tsare da su.

Haka kuma su kan kai hari ne a sauran kananan hukumomin da ba a kulla wannan yarjejeniya ta zaman lafiya da su ba, su yi barna su yi kisa su kwashe kayayyakin da jama’a.

Irin haka na ci gaba da faruwa, misali an yi zaman sulhu da barayin daji a karamar hukumar Kankara amma a satin da ya gabata rahotanni sun bayyana cewa an je an sace mutum 60 a garin Zango da Kankara.

Haka abin yake a karamar hukumar Faskari inda suka je garin Tafoki suka kwashe mashinan jama’a a ya yin da suke cikin gona suna aiki.

Sannan abubuwan da suka bayyana shine ana cigaba da kai hare-hare jefi-jefi kuma ana cigaba da satar jama’a da neman kudin fansa tare da sauran abubuwa marasa dad’i.

A bangaren barayin daji kuwa tuni harkoki suka fara kankama inda yanzu haka suke shigowa gari cin kasuwa da zuwa asibiti domin neman lafiyar su da ta iyalan su.

Ita ma gwamnatin jihar Katsina ta bada tabbacin cewa zata tallafawa wadanda wannan iftila’i ya shafa da jari da makarantu da asibitoci da sauran kayayyakin more rayuwa.

Gwamna Malam Dikko Umar Radda ya jaddada cewa hatta ‘yan bindigar da suka rungumi zaman lafiya za a taimaka masu da jari domin yin sana’a da za su dogara da kan su.

Gwamnan dai ya sha soka akan yadda rana tsaka ya yi mi’ara koma baya akan matsayar da ta cewa ba zai taba yin sulhu da barayin daji ba, sai dai idan ‘yan bindigar suka sha wuta suka mika kai.

Haka kuma daya daga hadiman gwamna Radda Jamilu Isma’il Mabai ya bayyana cewa ‘yan bindiga ne da kan su suka sha wuta daga jami’an tsaro suka nemi ayi sulhun ba gwamnati ba ce.

Sulhu
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Amince Da Ɗaukar Ma’aikatan Gandun Daji 1,000 Domin Matsalolin Tsaro A Katsina

MASU ALAKA

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa
Da ɗumi-ɗuminsa

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

July 10, 2026
An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa
Manyan Labarai

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

July 10, 2026
Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia
Labarai

Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia

July 10, 2026
Next Post
A Karo Na Hudu ’Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Yi Nasarar Kammala Ayyukansu A Wajen Kumbon

A Karo Na Hudu ’Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Yi Nasarar Kammala Ayyukansu A Wajen Kumbon

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon

Kasar Sin Ta Fitar Da Shirin Kai Wa Matakin Koli Na Fitar Da Hayakin Carbon

July 10, 2026
Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B

Sin Ta Yi Nasarar Dawo Da Rokar Da Ake Sarrafa Dawowarta A Tashin Farko Na Samfurin Long March-10B

July 10, 2026
CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare

CMG Ya Gabatar Da Shiri Na Musamman Mai Taken “Samun Nasara Dangane Da AI+” A Ketare

July 10, 2026
Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

Zargin Da Wasu Sassa Ke Yiwa Kasar Sin Na Takure Sauran Kasashe Masu Tasowa Ba Shi da Tushe Ko Makama

July 10, 2026
2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

2027: Tinubu Ya Sake Zaɓar Shettima A Matsayin Abokin Takararsa

July 10, 2026
Taron Kara Wa Juna Sani Na Duniya Ya Yi Nazari Kan Kwarewar Kasar Sin Wajen Rage Talauci

Taron Kara Wa Juna Sani Na Duniya Ya Yi Nazari Kan Kwarewar Kasar Sin Wajen Rage Talauci

July 10, 2026
An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

An Ceto Dukkanin Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Jihar Oyo — Fadar Shugaban Ƙasa

July 10, 2026
Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia

Xi Ya Zanta Da Shugabar Namibia

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ko Ka San Dalilin Da Ya Sa Chana Da Indiya Ba Sa Buga Kofin Duniya?

July 10, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.