• English
  • Business News
Friday, October 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sulhu Da ‘Yan Bindiga: Gwamna Lawal Ya Mai Da Martani Ga Ministan Labarai

Ya ce Suna Da Hujjojin Da Ke Fallasa Jami'an Gwamnatin Tarayya Kan Sulhun

by Leadership Hausa
2 years ago
yan bindiga

Gwamna Dauda Lawal, ya mayar da martani ga Ministan Labarai, Mohammed Malagi kan batun sulhun da ake yi cikin sirri da ‘yan bindiga.

 Ya ce Gwamnatin Zamfara tana da gamsassun hujjoji da ke fallasa wasu jami’an Gwamnatin Tarayya da hannu dumu-dumu a shirya zaman sulhu da ‘yan bindiga.

A jiya ne Ministan na Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Malagi ya zargi Gwamnatin Zamfara da siyasantar da lamarin tsaro. Biyo bayan neman ƙarin bayani da Gwamna Dauda ya yi kan zargin zaman sulhu ta ƙarƙashin ƙasa da ‘yan bindiga.

  • Wa Ya Yi Sulhu Da ‘Yan Bindiga A Katsina?
  • Kotu Ta Umarci G-Fresh Da Ya Yi Bikon Matarsa Sayyada Sadiya Haruna

A wata takardar manema labarai, mai magana da yawun Gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya bayyana cewa Gwamnatin Dauda Lawal tana da hujjoji masu tayar da hankali da ke fallasa wasu jami’an Gwamnatin Tarayya kan sulhu da ‘yan bindiga.

Ya ƙara da cewa Ministan na Labarai ya yi ri-ga mallam masallaci wurin yanke hukunci tare da yankewa gwamnatin Zamfara hanzari.

LABARAI MASU NASABA

Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja

Afuwar Tinubu Ga Masu Manyan Laifuka: Ta Bar Baya Da Ƙura

Sanarwar ta ci gaba da cewa: “Mun nemi ƙarin bayani daga Gwamnatin Tarayya kan zaman sirri na sulhu da wasu jami’anta suke jagoranta a Zamfara ba tare da sanin Gwamnatin Jiha ko shugabanni jami’an tsaron jihar ba.

“Muna da gamsassun hujjoji dake tabbatar da wannan zaman sulhu tsakanin jami’an Gwamnatin Tarayya da ‘yan bindiga a wurare mabambanta a Zamfara.

“Akwai ban takaici a ce Ministan Yaɗa Labarai zai fito bainar jama’a ya kore batun ba tare da ya nemi sani daga jami’an tsaro ko ‘yan uwanshi da ke da hannu dumu – dumu a lamarin ba. Mun tsammaci tunda ƙwararre ne a harka watsa labarai, zai bi matakan da ilimi ya sharɗanta don tabbatarwa ko kore batun namu.

“Gwamnatin Jihar Zamfara tana matuƙar mutunta ƙa’ida tare da ganin ƙimar hukuma. Ba za mu fito kafafen watsa labarai muna fallasa sunayen jami’an Gwamnatin Tarayyan da ke wannan ta’asa ba, amma mun sanar da ‘yan Nijeriya don su nemi ƙarin bayani daga Gwamnatin ta Tarayya.

“Muna so mu sanar da Minista cewa jami’ansu na Gwamnatin Tarayya da ke jagorantar wannan zaman sulhu da ‘yan bindiga, sune ke siyasantar da matsalar tsaro, ba Gwamnatin Zamfara ba.

“Ba mu san daga inda Ministan ya samu ƙwarin gwiwan bugun ƙirji ya ce babu wani zaman sulhu da aka yi a Zamfara ba, saboda ai mun bayyana wuraren da aka yi waɗannan zama, irinsu Birnin Magaji, Maradun, Mun Haye, Ajah, Bawo, da kuma Bagege.

“Muna sake nanatawa cewa sulhu da ‘yan bindiga a Zamfara ba zai taɓa haifar da ɗa mai ido ba. Sam! Ba wannan ba ne mafita ga matsalar, a yi amfani da qarfi kawai a kauda su, wanna ita ce matsayarmu har gobe.

“Muna kira ga Gwamnatin Tarayya da ta daina biye wa ‘yan amshin Shata, ta yi bincike tare da wanke kanta daga aikin waɗannan dillalan sulhu da ‘yan bindiga.” In ji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja
Manyan Labarai

Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja

October 17, 2025
Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja
Manyan Labarai

Afuwar Tinubu Ga Masu Manyan Laifuka: Ta Bar Baya Da Ƙura

October 17, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Shugaban Ƙasa Zai Sake Nazari Kan Mutanen Da Aka Yi Wa Afuwa

October 16, 2025
Next Post
Saudiyya

Bikin Kafuwar Daular Saudiyya Shekara 93: Abubuwan Da Suka Kamata A Sani

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Kasar Sin: Sin Za Ta Kyautata Matakan Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Kasar Sin: Sin Za Ta Kyautata Matakan Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth

October 17, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

Zan Tabbatar Ana Tafiyar Da Ayyuka A Tashoshin Jiragen Ruwa A Afrika Ta Yamma —Dantsoho

October 17, 2025
Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja

Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja

October 17, 2025
peter

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
Ƙungiyar NNYLF Ta Gargaɗi Atiku Da Sowore Kan Cinna Wutar Rikici A Nijeriya

Ƙungiyar NNYLF Ta Gargaɗi Atiku Da Sowore Kan Cinna Wutar Rikici A Nijeriya

October 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilin Karyewar Farashin Kayan Abinci

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilin Karyewar Farashin Kayan Abinci

October 17, 2025
Tinubu

Batun Yin Afuwa Ga ‘Yan Yankin Ogoni Huɗu

October 17, 2025
Shettima

‘Yan Nijeriya Na Dab Da Fita Daga Halin Kuncin Talauci – Shettima 

October 17, 2025
Manzon Allah

Manzon Allah (SAW) Ne Ya Kafa Tushen Wayewar Kai A Duniya

October 17, 2025
An Kashe Mutane Da Dama Da Kone Gidajensu A Wani Hari Da Aka Kai Benuwai

Yadda ‘Yan Bindiga Ke Zafafa Hare-hare A Jihohin Arewa Maso Yamma

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.