Wata kotun shari’ar musulunci da ke zamanta a filin hoki da ke babban birnin Kano, ta umarci Abubakar Ibrahim da aka fi sani da G-Fresh, da ya koma gida ya shirya zuwa wajen bikon matarsa da ta yi yaji.
Kotun wadda ta bayyana cewar, tunda shi G-Fresh bai saki matarsa ba, akwai bukatar ya yi bikon ta domin cigaba da zaman aurensu.
Lauyar G-Fresh, Barr Fatima Aliyu ta bayyana cewa, har yanzun wanda ta ke karewa na matukar kaunar matarsa wanda hakan yasa ba zai iya rabuwa da ita ba.
Talla
Kotun dai ta umurci G-Fresh 25 ga watan Satumba zuwa 10 ga watan Oktoba da ya sulhunta da matarsa, Sayyada Sadiya Haruna.
Talla