• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ta Yaya Za a Ba Matasa Damar Raya Kansu?

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 months ago
Matasa

Hausawa su kan ce “Karen bana shi ke maganin zomon bana”, don nuna cewa matasa ne suke iya daidaita matsalolin da ake fuskanta a zamanin da muke ciki. A duk lokacin da na tuna da maganar da wani abokina dan Najeriya, ya kan ce, “Matasa su ma sun haifar da dimbin matsaloli”. To, a ganina, wadannan matasa dama kawai suke bukata ta raya kansu, da nuna kwarewarsu.

 

A kwanan baya, kasar Sin ta gudanar da wata gasar daliban jami’o’i ta fuskar kirkiro sabbin fasahohi, a kasar Kenya, wadda ta zama wata kyakkyawar dama ga matasan kasashen Afirka. A wajen gasar da jami’ar koyon ilimin noma ta birnin Nanjing na kasar Sin ta karbi bakuncinta, wasu tawagogi 30 daga jami’o’i 21 na kasashe 9 dake nahiyar Afirka sun samu lambobin yabo.

  • Nijeriya Da Indiya Za Su Haɗa Kai Wajen Yaƙi Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi
  • Al Hilal Za Ta Biya Yuro Miliyan 53 Don Ɗaukar Nunez Daga Liverpool

Cikin abubuwan da aka kirkiro wadanda suka samu lambar yabo, akwai wani sabon nau’in leda da ake amfani da ita wajen rufe gonaki don adana ruwa a cikin kasa, da wasu dalibai ‘yan kasar Kenya suka kirkira; da wata sabuwar fasahar samar da sabon nau’in tumatir da ya dace da muhallin kasashen Afirka, da wasu daliban kasar Tanzania suka tsara. Ban da haka kuma, akwai inji mai sarrafa kansa wanda ke iya bambanta kunshin sakonni da kuma raba su, da wasu dalibai na kasar Habasha suka tsara; gami da wani sabon nau’in abincin kaza mai matukar araha, da wasu daliban kasar Ghana suka kirkira, da dai sauransu. Ta hanyar dandalin da kasar Sin ta samar, wadannan matasan kasashen Afirka sun nuna hazakarsu, tare da samar da gudunmowa ga yunkurin raya kimiyya da fasaha a nahiyar Afirka.

Sa’an nan, hakika idan mun yi tunani kan abun da ya sa aka shirya gasar, to, za mu fahimci cewa, hadin gwiwar Sin da Afirka wata kyakkyawar dama ce ga matasan kasashen Afirka, a fannin raya kansu.

LABARAI MASU NASABA

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

Mun san cewa, ci gaban harkokin matasa na bukatar bunkasar sana’o’i. Cikin shekarun nan, aikin zuba jari ga kasashen Afirka da kasar Sin ke yi na samun ci gaba yadda ake bukata. Inda yawan kudin da Sin take zubawa kai tsaye a fannin samar da kayayyaki a kasashen Afirka, ya kai fiye da dalar Amurka miliyan 400 a duk shekara. Kana darajar hadin kan bangarorin Afirka da Sin ta fuskar gina kayayyakin more rayuwa, ta kai fiye da dala biliyan 37 a duk shekara. Hadin gwiwar bangarorin 2 ya shafi zirga-zirgar ababen hawa, da aikin gona, da makamashi, da tattalin arziki mai alaka da fasahohin zamani, da fasahohin bunkasa tattalin arziki ba tare da gurbata muhalli ba, da dai sauransu, ta yadda ya taimaki kokarin raya masana’antu da habaka tsarin tattalin arziki zuwa fannoni daban daban a kasashen Afirka, da samar da dimbin guraben aikin yi, gami da damammakin raya sana’o’i ga matasan kasashen.

Ban da haka, ci gaban harkokin matasa ba zai rasa alaka da karuwar ilimi da ingantuwar fasahohi ba, inda a wannan fanni ma kasar Sin ta tsara ayyukan hadin kai da yawa, don samar da damammakin samun horon fasahohin sana’o’i ga dimbin matasan Afirka, da horar da kwararrun masana matasa masu ilimin aikin gona da masu jagorantar aikin wadatar da manoma ta wasu sabbin fasahohi a kasashen Afirka, da kafa cibiyoyin bude sabbin kamfanoni da kirkiro sabbin fasahohi na matasa, da kulla huldar hadin kai tsakanin jami’o’i dari 1 na kasashen Afirka da kasar Sin, da dai sauransu. Inda gasar da muka ambata ita ma take cikin ayyukan da aka tsara tare da aiwatar da su.

Sande Ngalande, darakta ne na cibiyar nazarin batutuwa masu alaka da shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya” ta jami’ar Zambia. Ya taba bayyana cewa, dabarar kasar Sin ta zamanantar da kasa ta amfani kasashen Afirka, inda dimbin matasan Afirka masu sana’o’i daban daban ke son mu’ammala da Sin, da fahimtar Sin, da koyon fasahohin kasar Sin. Kana ta hanyar hadin gwiwar Sin da Afirka, matasan Afirka suna iya kulla zumunci mai zurfi da Sinawa, gami da samun damar raya kansu, da kasashensu, da tabbatar da ci gaba mai dorewa a nahiyar Afirka.

Cikin shirin ajandar shekarar 2063 na kungiyar kasashen Afirka ta AU, an ce ya kamata a sanya matasa su zama karfin farfado da nahiyar Afirka, kuma hadin gwiwar Sin da Afirka na taimakawa wajen ganin tabbatuwar wannan buri a zahiri. (Bello Wang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki
Ra'ayi Riga

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 4, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan
Ra'ayi Riga

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

November 4, 2025
A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?
Ra'ayi Riga

A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya?

November 2, 2025
Next Post
Gwamnan Kano Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Gentle, Ya Bada Umarnin Zakulo Masu Laifin

Gwamnan Kano Ya Yi Ta'aziyyar Rasuwar Gentle, Ya Bada Umarnin Zakulo Masu Laifin

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025
tinubu

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025
Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

November 4, 2025
2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

November 4, 2025
Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

November 4, 2025
Karancin Abinci: Kofar Ofishin Tinubu A Rufe Take, Har Wasu Ministoci Ba Su Iya Ganinsa – Ndume 

Zargin Kisan Kiyashi Ga Kiristoci: Trump Bai San Ƙalubalen Tsaron Da Najeriya Ke Ciki Ba — Ndume

November 4, 2025
Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.