• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ta’addanci: Buhari Ya Jinjina Wa Nasarorin Da Sojojin Nijeriya Ke Samu

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Ta’addanci: Buhari Ya Jinjina Wa Nasarorin Da Sojojin Nijeriya Ke Samu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasa Muhammadu Buhari a ranar Alhamis a Jaji da ke jihar Kaduna ya jinjina tare da irin sadaukarwa gami da nasarorin da dakarun sojin kasar nan suke samu wajen kare kasar nan da kuma jajircewarsu.

Da yake jawabi a wajen yaye dalibai 247 na manyan kwas 44 ta Kwalejin horar da jami’an soji da ke Jaji, shugaba ta cikin sanarwar da hadiminsa Garba Shehu ya fitar, Buhari ya sha alwashin cewa, gwamnatinsa za ta cigaba da samar wa dakarun Sojoji abubuwan da suke bukata na goyon baya wajen cigaba da yakar ‘yan ta’adda da ta’addanci.

  • Karya Fure Take Ba Ta ’Ya’ya

‘‘Sojojin Nijeriya su na aiki tukuru da kwarewa da gogewar da suke da su wajen shafe barazanar tsaro da kare kasar nan.

“Kokarin sojojin kasa na yaki da ‘yan Boko Haram, ‘yan bindiga, masu garkuwa da mutane, da sauran matsalolin tsaro abun jinjina da yabawa ne. Tababs sojojin mu na kokari.

“Wannan Gwamnatin za ta ci gaba da samar da dukkanin abubuwan da Sojoji ke bukata da goya musu baya domin cimma nasarorin da aka sanya a gaba,” ya shaida.

Labarai Masu Nasaba

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

Shugaban ya ce matsalolin tsaro da ake fama da shi a duniya baki daya ma na samo asali ne bisa dalilai daban-daban. Don haka ya ce akwai bukatar kara sanya tsaro a iyakokin kasar nan domin dakile aniyar ‘yan ta’adda.

Daga bisani ya taya wadanda aka yaye murna tare da jawo hankalinsu da su bada tasu gudunmawar wajen kare kasar nan a kowani lokaci.

A jawabinsa na maraba, Kwamandan Kwalejin, Air Vice Marshall (AVM) Olurotimi Tuwase, ya yi bayanin cewa sojoji 111 ne, 69 sojojin ruwa ne, 42 kuma Sojoji sama ne, da kuma wasu karin daliban da aka yaye da suka samu horo daban-daban ciki har da dalibai daga kasashen waje.

AVM Tuwase ya kara da cewa, daliban da aka yaye kan kwas din 44 sun fito daga kasashen Burkina Faso, Cameroun, Chad, The Gambia, Ghana, Liberia, Mali, Niger, Rwanda, Sierra Leone, Tanzania, Togo da Zambia.

Kwamandan ya gode wa shugaban kasa Buhari a bisa irin goyon bayan da yake basu da karfafawa musu guiwa a kowani lokaci.

A wajen taron Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya mika lambar yabo ga daliban da suka yi zarra a cikin wadanda aka yaye din.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaba Xi Ya Aike Da Sakon Ta’aziyyar Tsohon Shugaban Kasar Angola 

Next Post

SABC: Alakar Moriyar Juna Dake Tsakanin Sin Da Afirka Ta Samu Yabo

Related

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba
Da É—umi-É—uminsa

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

3 hours ago
‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas
Manyan Labarai

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

5 hours ago
Yajin Aikin ASUU Na Barazana Ga Ci Gaban Kasa
Labarai

ASUU Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Rashin Cika Mata Alƙawura

7 hours ago
Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka
Ra'ayi Riga

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

7 hours ago
Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya
Rahotonni

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

10 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

19 hours ago
Next Post
SABC: Alakar Moriyar Juna Dake Tsakanin Sin Da Afirka Ta Samu Yabo

SABC: Alakar Moriyar Juna Dake Tsakanin Sin Da Afirka Ta Samu Yabo

LABARAI MASU NASABA

Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC

Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC

August 26, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harbar Rukunonin Taurarin Dan Adam 10 

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harbar Rukunonin Taurarin Dan Adam 10 

August 26, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

August 26, 2025
Saka Zai Yi Jinyar Makonni 4 Sakamakon Rauni Da Ya Samu A Wasan Leeds

Saka Zai Yi Jinyar Makonni 4 Sakamakon Rauni Da Ya Samu A Wasan Leeds

August 26, 2025
‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

August 26, 2025
ÆŠaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci

ÆŠaruruwan ‘Yan APC Sun Koma ADC A Sakkwato Saboda Rashin Tsaro Da Talauci

August 26, 2025
Yajin Aikin ASUU Na Barazana Ga Ci Gaban Kasa

ASUU Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Rashin Cika Mata Alƙawura

August 26, 2025
Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

Ranar Hausa Ta Duniya: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

August 26, 2025
ÆŠan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

ÆŠan Nijeriya Ya Lashe Lambar Azurfa A Gasar Ninkaya Ta Duniya

August 26, 2025
Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.