• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tabbas Mun Samu Tangarda Wurin Shigar Da Sakamakon Zaben 2023 –INEC

byYusuf Shuaibu
2 years ago
INEC

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta bayyana cewa tabbas ta samu matsala wurin saka sakamakon zaben shugaban kasa a na’ura, sannan kuma ba ta samu wani taimakon kuda ba daga wurin kowa sai dai gwamnatin tarayya wacce ita ce doka ya daura mata alhakkin yin hakan.

Shughaban hukumar INEC, Farfesa Mahmood Yakubu shi ya bayyana hakan a yayin da yake bayar da ba’asi kan na’urar da aka yi amfani da su a lokacin zaben 2023, a lokacin da yake yi wa kungiyoyin fararen huda bayanai kan nazarin zaben 2023.

  • ’Yan Bindiga Sun Kashe Shugaban JIBWIS, Sun Sace Mutane 50 A Kaduna
  • Badakala A Kano: An Gano Biliyan 4 Da Ta Yi Batan-Dabo A KASCO

Ya kara jaddada cewa abokan hulda sun bayar da tallafi ne kai tsaye ta hanyar kungiyoyin fararen huda wajen gudanar da ayyukan zabe.

Shugaban INEC ya gode wa kungiyoyin farar hula da abokan huda ci bisa gagarumin goyon bayan da suka bai wa hukumar a zaben 2023.

Shugaban na INEC ya tunatar da cewa, kungiyoyi 228 (na gida 190 da 38 na kasashen waje) aka amince da su a matsayin masu sanya ido a zaben da ya gabata, 67 ne kawai suka mika rahotonsu ga hukumar kan zabe.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

Ya ce: “A kan wannan lamari, ya dace hukumar ta nuna jin dadinta ga kungiyoyin farar hula da abokan hulda bisa gagarumin goyon bayan da suke bai wa hukumar a lokacin zaben 2023.

Wannan ya zo ne ta hanyar shawarwarin kan fasahar sadarwa da ilimantar da masu jefa kuri’a da gudanar da tarurruka da taron kara wa juna sani da kuma buga takardu.

“A wannan hadin gwiwar ne hukumar ta tantance masu sa ido saboda samun jin ra’ayoyi kan zabe da kuma shawarwarin da suka dace wadanda suke taimaka sosai wajen gudanar da zabe. Domin a zaben shekarar 2023, hukumar ta samu korafe-korafe guda 538 (504 na cikin gida da 34 na kasashen waje) daga wurin masu sa ido. Bayan yin cikakken nazari kan korafe-korafen, kungiyoyi 228 ne kawai (190 na cikin gida da 38 na waje) suka cika ka’idodin da aka zayyana. Sai dai kawo yanzu kungiyoyin sa ido 67 ne (62 na cikin gida da kuma na kasashen waje biyar) suka gabatar da rahoton bincikensu wanda ke wakiltar kusan kashi 30 na kungiyoyin da aka amince da su a zaben. Muna kira ga duk sauran kungiyoyin sa ido da aka amince da su wadanda har yanzu ba su gabatar da rahotonsu ba su yi kokarin gabatar wa hukumar.”

Shugaban INEC ya bayyana cewa an samu nasarar tantance masu kada kuri’a ta hanyar amfani da na’urar BBAS, amma kuma an samu matsala wajen shigar da sakamakon zabe ta intanet ta wannan na’ura.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

October 3, 2025
Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar
Tambarin Dimokuradiyya

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

October 3, 2025
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

September 27, 2025
Next Post
Yajin aiki: Tinubu Ya Roki Kungiyar Kwadago Da Ta Dan Kara Masa Lokaci

Tinubu Zai Karrama Matar Da Ta Tsinci Dala 80,000 Ta Mayar A Makka

LABARAI MASU NASABA

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version