ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tabbas Mun Samu Tangarda Wurin Shigar Da Sakamakon Zaben 2023 –INEC

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
INEC

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta bayyana cewa tabbas ta samu matsala wurin saka sakamakon zaben shugaban kasa a na’ura, sannan kuma ba ta samu wani taimakon kuda ba daga wurin kowa sai dai gwamnatin tarayya wacce ita ce doka ya daura mata alhakkin yin hakan.

Shughaban hukumar INEC, Farfesa Mahmood Yakubu shi ya bayyana hakan a yayin da yake bayar da ba’asi kan na’urar da aka yi amfani da su a lokacin zaben 2023, a lokacin da yake yi wa kungiyoyin fararen huda bayanai kan nazarin zaben 2023.

  • ’Yan Bindiga Sun Kashe Shugaban JIBWIS, Sun Sace Mutane 50 A Kaduna
  • Badakala A Kano: An Gano Biliyan 4 Da Ta Yi Batan-Dabo A KASCO

Ya kara jaddada cewa abokan hulda sun bayar da tallafi ne kai tsaye ta hanyar kungiyoyin fararen huda wajen gudanar da ayyukan zabe.

ADVERTISEMENT

Shugaban INEC ya gode wa kungiyoyin farar hula da abokan huda ci bisa gagarumin goyon bayan da suka bai wa hukumar a zaben 2023.

Shugaban na INEC ya tunatar da cewa, kungiyoyi 228 (na gida 190 da 38 na kasashen waje) aka amince da su a matsayin masu sanya ido a zaben da ya gabata, 67 ne kawai suka mika rahotonsu ga hukumar kan zabe.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ya ce: “A kan wannan lamari, ya dace hukumar ta nuna jin dadinta ga kungiyoyin farar hula da abokan hulda bisa gagarumin goyon bayan da suke bai wa hukumar a lokacin zaben 2023.

Wannan ya zo ne ta hanyar shawarwarin kan fasahar sadarwa da ilimantar da masu jefa kuri’a da gudanar da tarurruka da taron kara wa juna sani da kuma buga takardu.

“A wannan hadin gwiwar ne hukumar ta tantance masu sa ido saboda samun jin ra’ayoyi kan zabe da kuma shawarwarin da suka dace wadanda suke taimaka sosai wajen gudanar da zabe. Domin a zaben shekarar 2023, hukumar ta samu korafe-korafe guda 538 (504 na cikin gida da 34 na kasashen waje) daga wurin masu sa ido. Bayan yin cikakken nazari kan korafe-korafen, kungiyoyi 228 ne kawai (190 na cikin gida da 38 na waje) suka cika ka’idodin da aka zayyana. Sai dai kawo yanzu kungiyoyin sa ido 67 ne (62 na cikin gida da kuma na kasashen waje biyar) suka gabatar da rahoton bincikensu wanda ke wakiltar kusan kashi 30 na kungiyoyin da aka amince da su a zaben. Muna kira ga duk sauran kungiyoyin sa ido da aka amince da su wadanda har yanzu ba su gabatar da rahotonsu ba su yi kokarin gabatar wa hukumar.”

Shugaban INEC ya bayyana cewa an samu nasarar tantance masu kada kuri’a ta hanyar amfani da na’urar BBAS, amma kuma an samu matsala wajen shigar da sakamakon zabe ta intanet ta wannan na’ura.

INEC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Hukuncin Kotu Na Barazana Ga Zaben 2027 —INEC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

MASU ALAKA

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Fitar Da Gwani Na APC: Tinubu Zai Shiga Tsakani Wajen Warware Rikicin Jam’iyyar

June 5, 2026
Next Post
Yajin aiki: Tinubu Ya Roki Kungiyar Kwadago Da Ta Dan Kara Masa Lokaci

Tinubu Zai Karrama Matar Da Ta Tsinci Dala 80,000 Ta Mayar A Makka

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.