• English
  • Business News
Sunday, August 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tabbatuwar Zaman Lafiya A Duniya Na Bukatar Hadin Gwiwa Da Cudanyar Bangarori Daban-daban

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Zaman lafiya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A jiya Litinin ne mataimakin wakilin dindindin na kasar Sin a MDD Dai Bing, ya jaddada bukatar mambobin Kwamitin Sulhu na MDD, su tsaya tsayin daka kan ruhin hadin gwiwa.

Wannan kira ya zo a lokaci mafi muhimmanci la’akari da yanayin da duniya ke ciki. Babban makasudin MDD shi ne dinke baraka da tabbatar da hadin kan kasa da kasa bisa adalci da girmama juna. Haka kuma batun yake ga duk wasu sassa dake karkashin majalisar, ciki har da Kwamitin Sulhu, wanda nauyin tabbatar da sulhu da tsaro a kasa da kasa ya rataya a wuyansa.

  • Salon Dimokuradiyya Mai Sigar Musamman Ta Kasar Sin 
  • Xi Ya Tattauna Harkokin Kasa Tare Da Wakilai Da Mambobin Manyan Taruka Biyu Na Kasar Sin

Batun zaman lafiya da tsaro bai kamata ya zama wani abu da za a siyasantar ba, domin ya shafi rayuka da dukiyoyin jama’a. Ya kamata tabbatar da tsaron rayukan jama’a ya kasance wani abu da ya sha gaban komai, haka kuma, bai kamata a rika amfani da shi a matsayin makami ba.

Yanayin da duniya ta shigha yanzu haka, inda ake fuskantar rigin-ginmu, ya dace ya zaburar da kasashen duniya cewa, ana tsananin bukatar hadin gwiwa da kira da murya daya domin kare rayukan jama’a da tabbatar da kwanciyar hankalin duniya.

Kamar yadda Jakadan na Sin ya bayyana, gabatar da daftari, nauyi ne maimakon wata dama. Nauyi ne da ya rataya a kan kasashen na tabbatar da sun yi abun da ya dace cikin adalci da hangen nesa da sanin ya kamata, ba wai amfani da shi a matsayin dama ta siyasa ba. Ran bil adama, abu ne mai daraja, bai kyautu a rika sanya siyasa cikin duk wata harka da ta shafi ceton rai ko rayuka ba. Yadda ake amfani kujerar dindin din a matsayin dama ko kuma makamin siyasa a MDD, ya kara ta’azzara lamuran a duniya, maimakon tsagaita bude wuta da cimma sulhu, ana ta zubar da jini da asarar rayuka da dukiyoyi.

Labarai Masu Nasaba

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Kamar yadda kasar Sin take kira a kullum, tabbatar da zaman lafiya a duniya na bukatar hadin gwiwa da cudanyar bangarori daban-daban. Bugu da kari, kamata ya yi kasa da kasa, musammam manya su yi koyi tare da amincewa da wannan ra’ayi na kasar Sin, wato ra’ayin tabbatar da adalci da zaman lafiya da hadin gwiwa da kuma tsayawa kasashe masu tasowa da goya musu baya. (Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Anambra Ta Rusa Shaguna 2,000 A Onitsa

Next Post

SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 2

Related

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan
Daga Birnin Sin

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

1 day ago
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar
Daga Birnin Sin

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

1 day ago
Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 
Daga Birnin Sin

Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

1 day ago
Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika
Daga Birnin Sin

Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

1 day ago
Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150
Daga Birnin Sin

Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

1 day ago
Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

2 days ago
Next Post
SAHUR [Falalarsa Da Fa’idojinsa] Na 1

SAHUR [Falalarsa Da Fa'idojinsa] Na 2

LABARAI MASU NASABA

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

August 10, 2025
Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

Ƴansanda Sun Kama Makashin Wani Ɗan Jarida A Abuja Bayan Shekara Ɗaya

August 10, 2025
Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

Fa’ida Da Muhimmancin Tattalin Lokaci Ga Ɗan’adam

August 10, 2025
INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

August 10, 2025
Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

August 10, 2025
Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara

Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara

August 10, 2025
Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas

Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas

August 10, 2025
Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi

Yadda Jinkirin Tabbatar Da ‘Yancin Cin Gashin Kai Ke Cutar Da Ma’aikatan Ƙananan Hukumomi

August 10, 2025
Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

Gwamna Abba Ya Bai Wa Dalibai 1,130 Kayan Aikin Sana’o’in Hannu

August 10, 2025
NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 

NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 

August 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.