• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taimkon Juna Tushen Dangantakar Sin Da Afrika

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Taimkon Juna Tushen Dangantakar Sin Da Afrika
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A farkon wannan mako ne shugaban kasar Eritrea Isaias Afwerki ya fara ziyarar aiki a kasar Sin, inda da yammacin jiya agogon Beijing, ya gana da shugaban kasar Sin Xi Jinping.

A ranar 24 ga wannan wata ne za a cika shekaru 30 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin Sin da Eritrea, wanda ke tabbatar da irin dadaddiyar huldar dake tsakaninsu.

  • Hadin Gwiwa Da Kasar Sin Zai Bunkasa Ayyukan Masana’antu A Afrika

Da yake jawabi yayin ganawarsa da takwaransa na Eritrea, shugaban kasar Sin ya ce, ba tare da la’akari da yadda yanayin duniya zai kasance a nan gaba ba, mutunta juna da goyon baya da taimako, su ne za su kasance tubalin abota tsakanin Sin da Kasashen Afrika.

Idan ana batun mutunta juna, to ba shakka kasar Sin ta kasance mai mutunta ikon mulki da cikakken ’yancin kasashen Afrika, domin ta kasance kasar da ta samu ci gaba ba tare da bautar da su ko ci da guminsu ba, haka kuma ba ta yi musu katsalandan cikin harkokinsu na gida.

A ko da yaushe, kasar Sin ta kan nuna girmamawa da kwarin gwiwarta kan karfin kasashen Afrika, inda take bayyana cewa, al’ummar Afrika su suka san matsalolinsu, kuma su ne za su iya samar da mafita, wannan hali ne na dattako da sanin ya kamata. Har ila yau, ita ce mai karfafa musu gwiwar lalubo hanyoyin da suka dace da su na samun ci gaba, ba tare da arowa daga waje ba.

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Wannan ya nuna matsayinta na babbar kasa da kuma burinta na ganin sun tsaya da kafafunsu, sun samu ci gaba ba tare da dogaro da wasu bangarori da za su gindaya musu sharuda ko danne su ko kuma yi musu katsalandan ba.

Su ma a nasu bangare, mutuncin suke nunawa ta yadda suke amincewa da manufar kasancewar Sin daya tak a duniya, da goyon bayan matakan tabbatar da tsaro da take dauka a cikin gida da kuma kauracewa tsoma baki cikin harkokinta na cikin gida.
Taimako kuwa, ba zai misaltu ko ya kirgu ba. Ko a wannan lokaci da duniya ke fuskantar rashin tabbas da halin son kai daga manyan kasashe, kasar Sin ta tsaya kan bakanta na taimakawa kasashen Afrika.

Kama daga ababen more rayuwa, fasahohin ayyukan gona da kiwon lafiya da tsaro da cinikayya da sauransu. Kasar Sin tana bude kofarta ga kasashen Afrika domin su shigo su ci gajiyar babbar kasuwarta, haka kuma tana karfafawa kamfanoninta da masu zuba jari gwiwar shiga kasashen Afrika domin su zuba jari. A nasu bangare, kasashen Afrika sun kasance masu maraba da kayayyaki kirar kasar Sin da bude kofa ga kamfanonin da ’yan kasuwa Sinawa a kasashensu.

Nasarori da kyakkyawan tasirin dangantakar bangarorin biyu a bayyane yake, domin Sin da Afrika sun zarce abokai, sun koma ’yan uwa, su kasance masu martaba juna da cin moriyar juna da kuma neman ci gaba na bai daya, ba tare da son ganin faduwar daya daga cikinsu ba. (Faeza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Bayar Da Belin Dakta Idris Abdul’aziz Bisa Sharadi Uku

Next Post

Yanzu-yanzu: Shugaba Buhari Ya Dawo Nijeriya Daga Landan

Related

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su
Daga Birnin Sin

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

7 hours ago
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

8 hours ago
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko
Daga Birnin Sin

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

9 hours ago
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba
Daga Birnin Sin

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

10 hours ago
Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai
Daga Birnin Sin

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

11 hours ago
An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya
Daga Birnin Sin

An Watsa Shirin “Yawon Bude Ido A Tuscany” Da Cmg Ya Gabatar A Italiya

12 hours ago
Next Post
Yanzu-yanzu: Shugaba Buhari Ya Dawo Nijeriya Daga Landan

Yanzu-yanzu: Shugaba Buhari Ya Dawo Nijeriya Daga Landan

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

June 27, 2025
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

June 27, 2025
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

June 27, 2025
Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

June 27, 2025
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

June 27, 2025
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

June 27, 2025
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

June 27, 2025
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.