ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taimkon Juna Tushen Dangantakar Sin Da Afrika

by CMG Hausa
3 years ago
Sin

A farkon wannan mako ne shugaban kasar Eritrea Isaias Afwerki ya fara ziyarar aiki a kasar Sin, inda da yammacin jiya agogon Beijing, ya gana da shugaban kasar Sin Xi Jinping.

A ranar 24 ga wannan wata ne za a cika shekaru 30 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin Sin da Eritrea, wanda ke tabbatar da irin dadaddiyar huldar dake tsakaninsu.

  • Hadin Gwiwa Da Kasar Sin Zai Bunkasa Ayyukan Masana’antu A Afrika

Da yake jawabi yayin ganawarsa da takwaransa na Eritrea, shugaban kasar Sin ya ce, ba tare da la’akari da yadda yanayin duniya zai kasance a nan gaba ba, mutunta juna da goyon baya da taimako, su ne za su kasance tubalin abota tsakanin Sin da Kasashen Afrika.

ADVERTISEMENT

Idan ana batun mutunta juna, to ba shakka kasar Sin ta kasance mai mutunta ikon mulki da cikakken ’yancin kasashen Afrika, domin ta kasance kasar da ta samu ci gaba ba tare da bautar da su ko ci da guminsu ba, haka kuma ba ta yi musu katsalandan cikin harkokinsu na gida.

A ko da yaushe, kasar Sin ta kan nuna girmamawa da kwarin gwiwarta kan karfin kasashen Afrika, inda take bayyana cewa, al’ummar Afrika su suka san matsalolinsu, kuma su ne za su iya samar da mafita, wannan hali ne na dattako da sanin ya kamata. Har ila yau, ita ce mai karfafa musu gwiwar lalubo hanyoyin da suka dace da su na samun ci gaba, ba tare da arowa daga waje ba.

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping: Zan Sadaukar Da Rayuwata Don Bautawa Jama’a

Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

Wannan ya nuna matsayinta na babbar kasa da kuma burinta na ganin sun tsaya da kafafunsu, sun samu ci gaba ba tare da dogaro da wasu bangarori da za su gindaya musu sharuda ko danne su ko kuma yi musu katsalandan ba.

Su ma a nasu bangare, mutuncin suke nunawa ta yadda suke amincewa da manufar kasancewar Sin daya tak a duniya, da goyon bayan matakan tabbatar da tsaro da take dauka a cikin gida da kuma kauracewa tsoma baki cikin harkokinta na cikin gida.
Taimako kuwa, ba zai misaltu ko ya kirgu ba. Ko a wannan lokaci da duniya ke fuskantar rashin tabbas da halin son kai daga manyan kasashe, kasar Sin ta tsaya kan bakanta na taimakawa kasashen Afrika.

Kama daga ababen more rayuwa, fasahohin ayyukan gona da kiwon lafiya da tsaro da cinikayya da sauransu. Kasar Sin tana bude kofarta ga kasashen Afrika domin su shigo su ci gajiyar babbar kasuwarta, haka kuma tana karfafawa kamfanoninta da masu zuba jari gwiwar shiga kasashen Afrika domin su zuba jari. A nasu bangare, kasashen Afrika sun kasance masu maraba da kayayyaki kirar kasar Sin da bude kofa ga kamfanonin da ’yan kasuwa Sinawa a kasashensu.

Nasarori da kyakkyawan tasirin dangantakar bangarorin biyu a bayyane yake, domin Sin da Afrika sun zarce abokai, sun koma ’yan uwa, su kasance masu martaba juna da cin moriyar juna da kuma neman ci gaba na bai daya, ba tare da son ganin faduwar daya daga cikinsu ba. (Faeza Mustapha)

Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Xi Jinping: Zan Sadaukar Da Rayuwata Don Bautawa Jama’a
Daga Birnin Sin

Xi Jinping: Zan Sadaukar Da Rayuwata Don Bautawa Jama’a

June 15, 2026
Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Jigilar Hajoji Ta Jiragen Kasa Na Gudana Bisa Daidaito A Kasar Sin

June 14, 2026
An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28
Daga Birnin Sin

An Bude Bikin Fina-Finan Kasa Da Kasa Na Shanghai Karo Na 28

June 14, 2026
Next Post
Yanzu-yanzu: Shugaba Buhari Ya Dawo Nijeriya Daga Landan

Yanzu-yanzu: Shugaba Buhari Ya Dawo Nijeriya Daga Landan

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Ɗora Alhakin Tashin Farashin Gas Kan Canjin Kuɗaɗen Waje da Sauransu

Gwamnati Ta Ɗora Alhakin Tashin Farashin Gas Kan Canjin Kuɗaɗen Waje da Sauransu

June 15, 2026
Tunisiyya Ta Sallami Kocinta Bayan Shan Kashi 5-1 A Wasan Farko Na Kofin Duniya

Tunisiyya Ta Sallami Kocinta Bayan Shan Kashi 5-1 A Wasan Farko Na Kofin Duniya

June 15, 2026
Kotu Ta Umarci INEC Ta Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu 4

Kotu Ta Umarci INEC Ta Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu 4

June 15, 2026
ADC Ta Zaɓi Amaechi A Matsayin Mataimakin Atiku A Zaɓen 2027

ADC Ta Zaɓi Amaechi A Matsayin Mataimakin Atiku A Zaɓen 2027

June 15, 2026
Xi Jinping: Zan Sadaukar Da Rayuwata Don Bautawa Jama’a

Xi Jinping: Zan Sadaukar Da Rayuwata Don Bautawa Jama’a

June 15, 2026
Annobar Ƙwalara Ta Kashe Mutane Biyar, 11 Sun Kamu A Filato

Annobar Ƙwalara Ta Kashe Mutane Biyar, 11 Sun Kamu A Filato

June 15, 2026
Farashin Mai Ya Fadi Rigis Bayan Amurka Da Iran Sun Sasanta Kan Mashigar Hormuz

Farashin Mai Ya Fadi Rigis Bayan Amurka Da Iran Sun Sasanta Kan Mashigar Hormuz

June 15, 2026
An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

June 15, 2026
An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

June 15, 2026
Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

June 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.