ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taimkon Juna Tushen Dangantakar Sin Da Afrika

by CMG Hausa
3 years ago
Sin

A farkon wannan mako ne shugaban kasar Eritrea Isaias Afwerki ya fara ziyarar aiki a kasar Sin, inda da yammacin jiya agogon Beijing, ya gana da shugaban kasar Sin Xi Jinping.

A ranar 24 ga wannan wata ne za a cika shekaru 30 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin Sin da Eritrea, wanda ke tabbatar da irin dadaddiyar huldar dake tsakaninsu.

  • Hadin Gwiwa Da Kasar Sin Zai Bunkasa Ayyukan Masana’antu A Afrika

Da yake jawabi yayin ganawarsa da takwaransa na Eritrea, shugaban kasar Sin ya ce, ba tare da la’akari da yadda yanayin duniya zai kasance a nan gaba ba, mutunta juna da goyon baya da taimako, su ne za su kasance tubalin abota tsakanin Sin da Kasashen Afrika.

ADVERTISEMENT

Idan ana batun mutunta juna, to ba shakka kasar Sin ta kasance mai mutunta ikon mulki da cikakken ’yancin kasashen Afrika, domin ta kasance kasar da ta samu ci gaba ba tare da bautar da su ko ci da guminsu ba, haka kuma ba ta yi musu katsalandan cikin harkokinsu na gida.

A ko da yaushe, kasar Sin ta kan nuna girmamawa da kwarin gwiwarta kan karfin kasashen Afrika, inda take bayyana cewa, al’ummar Afrika su suka san matsalolinsu, kuma su ne za su iya samar da mafita, wannan hali ne na dattako da sanin ya kamata. Har ila yau, ita ce mai karfafa musu gwiwar lalubo hanyoyin da suka dace da su na samun ci gaba, ba tare da arowa daga waje ba.

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Wannan ya nuna matsayinta na babbar kasa da kuma burinta na ganin sun tsaya da kafafunsu, sun samu ci gaba ba tare da dogaro da wasu bangarori da za su gindaya musu sharuda ko danne su ko kuma yi musu katsalandan ba.

Su ma a nasu bangare, mutuncin suke nunawa ta yadda suke amincewa da manufar kasancewar Sin daya tak a duniya, da goyon bayan matakan tabbatar da tsaro da take dauka a cikin gida da kuma kauracewa tsoma baki cikin harkokinta na cikin gida.
Taimako kuwa, ba zai misaltu ko ya kirgu ba. Ko a wannan lokaci da duniya ke fuskantar rashin tabbas da halin son kai daga manyan kasashe, kasar Sin ta tsaya kan bakanta na taimakawa kasashen Afrika.

Kama daga ababen more rayuwa, fasahohin ayyukan gona da kiwon lafiya da tsaro da cinikayya da sauransu. Kasar Sin tana bude kofarta ga kasashen Afrika domin su shigo su ci gajiyar babbar kasuwarta, haka kuma tana karfafawa kamfanoninta da masu zuba jari gwiwar shiga kasashen Afrika domin su zuba jari. A nasu bangare, kasashen Afrika sun kasance masu maraba da kayayyaki kirar kasar Sin da bude kofa ga kamfanonin da ’yan kasuwa Sinawa a kasashensu.

Nasarori da kyakkyawan tasirin dangantakar bangarorin biyu a bayyane yake, domin Sin da Afrika sun zarce abokai, sun koma ’yan uwa, su kasance masu martaba juna da cin moriyar juna da kuma neman ci gaba na bai daya, ba tare da son ganin faduwar daya daga cikinsu ba. (Faeza Mustapha)

Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
Daga Birnin Sin

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Next Post
Yanzu-yanzu: Shugaba Buhari Ya Dawo Nijeriya Daga Landan

Yanzu-yanzu: Shugaba Buhari Ya Dawo Nijeriya Daga Landan

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.