• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihi Zai Yi Tir Da Matakin Amurka Na Hawa Kujerar Na Ki Game Da Burin Tsagaita Wuta A Gaza

by CGTN Hausa and Sulaiman
10 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Tarihi Zai Yi Tir Da Matakin Amurka Na Hawa Kujerar Na Ki Game Da Burin Tsagaita Wuta A Gaza
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tun bayan da kasar Amurka ta sake hawa kujerar na ki game da kudurin da aka gabatar a zauren kwamitin tsaron MDD, don gane da gaggauta tsagaita wuta a Gaza a kwanan baya, masharhanta ke ta sukar wannan mataki na Amurka, wanda ko shakka babu ya kara ingiza alummar Gaza cikin karin tashin hankali da yanayi na rashin tabbas. 

 

Alal hakika, abun takaici ne ganin yadda mambobin kwamitin tsaron MDD har 14 suka nuna amincewa da wannan kuduri, amma Amurka ta yi fatali da wannan matsaya tasu, a wani yanayi mai ban takaici da haifar da koma baya, wanda zai wanzar da tashe-tashen hankula da ake gani a Gaza, sama da watanni 13 da sake barkewar rikicin yankin.

  • Akpabio Ya Karɓi Baƙuncin Dattawan Niger Delta, Karanta Abin da Suka Tattauna 
  • Gwamna Yusuf Ya Mika Motocin Bas Na CNG Guda 10 Ga Kungiyar NLC Reshen Kano

Idan mun waiwayi baya, za mu ga cewa Amurka ta hau kujerar na ki game da wani kudurin makamancin wannan a ranar 18 ga watan Oktoban bara, lokacin da tuni adadin fararen hula da suka rasu sakamakon rikicin Gaza ya kai kusan mutum 3,000. A karo na biyu da Amurka ta dauki wannan mataki, adadin fararen hular da hare-haren Israila ya hallaka a Gaza ya kai mutum 17,000. Haka dai Amurka ta ci gaba da daukar wannan mataki na hawa kujerar na ki game da kudurin gaggauta kawo karshen wannan rikici, har zuwa karo na 5, inda a ranar 18 ga watan Afrilun bana ta kara hawa kujerar na ki, a gabar da tuni adadin alummun Gaza da suka rasu sanadin wannan rikici suka karu zuwa mutum 34,000.

 

Labarai Masu Nasaba

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

A halin da ake ciki yanzu kuwa, wannan adadi ya kai kusan mutum 44,000, amma Amurka ba ta sauya matsaya ba. Hakika wannan lamari ne mai matukar bakanta ran duk wani mai hankali da kaunar zaman lafiya. Adadin mutum 44,000 ba dan kadan ba ne, ya kuma kunshi yara kanana, da mata masu renon jarirai, da masu daukar nauyin bukatun iyalai cikin magidanta, wadanda asarar ran ko wane daya daga cikinsu, ke haifar da tashin hankali da damuwa ta tsawon rayuwa ga zuriyarsa.

 

Don haka, na kan tambayi kai na, shin anya rayuwar Falasdinawa na da wata daraja a idanun gwamnatin Amurka kuwa? Ko Amurka na iya waiwayar wadannan alummu da idon rahama da tausayawa? Abun da na yi imani da shi, shi ne ko bayan kawo karshen wannan tashin hankali, tabbas tarihi zai ci gaba da tunawa da mummunar matsayar Amurka game da matakan nan da take dauka a yanzu, tare da yin tir da halin ko in kula da rayukan dubban Falasdinawa mazauna zirin Gaza. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Akpabio Ya Karɓi Baƙuncin Dattawan Niger Delta, Karanta Abin da Suka Tattauna 

Next Post

Daga Ƙarshe Dai Za A Gudanar da Ƙidayar Ƙasa A 2025

Related

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
Daga Birnin Sin

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

8 hours ago
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani
Daga Birnin Sin

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

9 hours ago
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

10 hours ago
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari
Daga Birnin Sin

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

11 hours ago
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi
Daga Birnin Sin

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

12 hours ago
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

14 hours ago
Next Post
Daga Ƙarshe Dai Za A Gudanar da Ƙidayar Ƙasa A 2025

Daga Ƙarshe Dai Za A Gudanar da Ƙidayar Ƙasa A 2025

LABARAI MASU NASABA

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.