• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihi Zai Yi Tir Da Matakin Amurka Na Hawa Kujerar Na Ki Game Da Burin Tsagaita Wuta A Gaza

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Tarihi Zai Yi Tir Da Matakin Amurka Na Hawa Kujerar Na Ki Game Da Burin Tsagaita Wuta A Gaza
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tun bayan da kasar Amurka ta sake hawa kujerar na ki game da kudurin da aka gabatar a zauren kwamitin tsaron MDD, don gane da gaggauta tsagaita wuta a Gaza a kwanan baya, masharhanta ke ta sukar wannan mataki na Amurka, wanda ko shakka babu ya kara ingiza alummar Gaza cikin karin tashin hankali da yanayi na rashin tabbas. 

 

Alal hakika, abun takaici ne ganin yadda mambobin kwamitin tsaron MDD har 14 suka nuna amincewa da wannan kuduri, amma Amurka ta yi fatali da wannan matsaya tasu, a wani yanayi mai ban takaici da haifar da koma baya, wanda zai wanzar da tashe-tashen hankula da ake gani a Gaza, sama da watanni 13 da sake barkewar rikicin yankin.

  • Akpabio Ya Karɓi Baƙuncin Dattawan Niger Delta, Karanta Abin da Suka Tattauna 
  • Gwamna Yusuf Ya Mika Motocin Bas Na CNG Guda 10 Ga Kungiyar NLC Reshen Kano

Idan mun waiwayi baya, za mu ga cewa Amurka ta hau kujerar na ki game da wani kudurin makamancin wannan a ranar 18 ga watan Oktoban bara, lokacin da tuni adadin fararen hula da suka rasu sakamakon rikicin Gaza ya kai kusan mutum 3,000. A karo na biyu da Amurka ta dauki wannan mataki, adadin fararen hular da hare-haren Israila ya hallaka a Gaza ya kai mutum 17,000. Haka dai Amurka ta ci gaba da daukar wannan mataki na hawa kujerar na ki game da kudurin gaggauta kawo karshen wannan rikici, har zuwa karo na 5, inda a ranar 18 ga watan Afrilun bana ta kara hawa kujerar na ki, a gabar da tuni adadin alummun Gaza da suka rasu sanadin wannan rikici suka karu zuwa mutum 34,000.

 

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

A halin da ake ciki yanzu kuwa, wannan adadi ya kai kusan mutum 44,000, amma Amurka ba ta sauya matsaya ba. Hakika wannan lamari ne mai matukar bakanta ran duk wani mai hankali da kaunar zaman lafiya. Adadin mutum 44,000 ba dan kadan ba ne, ya kuma kunshi yara kanana, da mata masu renon jarirai, da masu daukar nauyin bukatun iyalai cikin magidanta, wadanda asarar ran ko wane daya daga cikinsu, ke haifar da tashin hankali da damuwa ta tsawon rayuwa ga zuriyarsa.

 

Don haka, na kan tambayi kai na, shin anya rayuwar Falasdinawa na da wata daraja a idanun gwamnatin Amurka kuwa? Ko Amurka na iya waiwayar wadannan alummu da idon rahama da tausayawa? Abun da na yi imani da shi, shi ne ko bayan kawo karshen wannan tashin hankali, tabbas tarihi zai ci gaba da tunawa da mummunar matsayar Amurka game da matakan nan da take dauka a yanzu, tare da yin tir da halin ko in kula da rayukan dubban Falasdinawa mazauna zirin Gaza. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Akpabio Ya Karɓi Baƙuncin Dattawan Niger Delta, Karanta Abin da Suka Tattauna 

Next Post

Daga Ƙarshe Dai Za A Gudanar da Ƙidayar Ƙasa A 2025

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

13 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

13 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

15 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

18 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

19 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

20 hours ago
Next Post
Daga Ƙarshe Dai Za A Gudanar da Ƙidayar Ƙasa A 2025

Daga Ƙarshe Dai Za A Gudanar da Ƙidayar Ƙasa A 2025

LABARAI MASU NASABA

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.