• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihi Zai Yi Tir Da Matakin Amurka Na Hawa Kujerar Na Ki Game Da Burin Tsagaita Wuta A Gaza

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Tarihi Zai Yi Tir Da Matakin Amurka Na Hawa Kujerar Na Ki Game Da Burin Tsagaita Wuta A Gaza
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tun bayan da kasar Amurka ta sake hawa kujerar na ki game da kudurin da aka gabatar a zauren kwamitin tsaron MDD, don gane da gaggauta tsagaita wuta a Gaza a kwanan baya, masharhanta ke ta sukar wannan mataki na Amurka, wanda ko shakka babu ya kara ingiza alummar Gaza cikin karin tashin hankali da yanayi na rashin tabbas. 

 

Alal hakika, abun takaici ne ganin yadda mambobin kwamitin tsaron MDD har 14 suka nuna amincewa da wannan kuduri, amma Amurka ta yi fatali da wannan matsaya tasu, a wani yanayi mai ban takaici da haifar da koma baya, wanda zai wanzar da tashe-tashen hankula da ake gani a Gaza, sama da watanni 13 da sake barkewar rikicin yankin.

  • Akpabio Ya Karɓi Baƙuncin Dattawan Niger Delta, Karanta Abin da Suka Tattauna 
  • Gwamna Yusuf Ya Mika Motocin Bas Na CNG Guda 10 Ga Kungiyar NLC Reshen Kano

Idan mun waiwayi baya, za mu ga cewa Amurka ta hau kujerar na ki game da wani kudurin makamancin wannan a ranar 18 ga watan Oktoban bara, lokacin da tuni adadin fararen hula da suka rasu sakamakon rikicin Gaza ya kai kusan mutum 3,000. A karo na biyu da Amurka ta dauki wannan mataki, adadin fararen hular da hare-haren Israila ya hallaka a Gaza ya kai mutum 17,000. Haka dai Amurka ta ci gaba da daukar wannan mataki na hawa kujerar na ki game da kudurin gaggauta kawo karshen wannan rikici, har zuwa karo na 5, inda a ranar 18 ga watan Afrilun bana ta kara hawa kujerar na ki, a gabar da tuni adadin alummun Gaza da suka rasu sanadin wannan rikici suka karu zuwa mutum 34,000.

 

Labarai Masu Nasaba

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

A halin da ake ciki yanzu kuwa, wannan adadi ya kai kusan mutum 44,000, amma Amurka ba ta sauya matsaya ba. Hakika wannan lamari ne mai matukar bakanta ran duk wani mai hankali da kaunar zaman lafiya. Adadin mutum 44,000 ba dan kadan ba ne, ya kuma kunshi yara kanana, da mata masu renon jarirai, da masu daukar nauyin bukatun iyalai cikin magidanta, wadanda asarar ran ko wane daya daga cikinsu, ke haifar da tashin hankali da damuwa ta tsawon rayuwa ga zuriyarsa.

 

Don haka, na kan tambayi kai na, shin anya rayuwar Falasdinawa na da wata daraja a idanun gwamnatin Amurka kuwa? Ko Amurka na iya waiwayar wadannan alummu da idon rahama da tausayawa? Abun da na yi imani da shi, shi ne ko bayan kawo karshen wannan tashin hankali, tabbas tarihi zai ci gaba da tunawa da mummunar matsayar Amurka game da matakan nan da take dauka a yanzu, tare da yin tir da halin ko in kula da rayukan dubban Falasdinawa mazauna zirin Gaza. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Akpabio Ya Karɓi Baƙuncin Dattawan Niger Delta, Karanta Abin da Suka Tattauna 

Next Post

Daga Ƙarshe Dai Za A Gudanar da Ƙidayar Ƙasa A 2025

Related

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa
Daga Birnin Sin

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

22 minutes ago
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

18 hours ago
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata
Daga Birnin Sin

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

19 hours ago
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

21 hours ago
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya
Daga Birnin Sin

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

22 hours ago
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

1 day ago
Next Post
Daga Ƙarshe Dai Za A Gudanar da Ƙidayar Ƙasa A 2025

Daga Ƙarshe Dai Za A Gudanar da Ƙidayar Ƙasa A 2025

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.