ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihi Zai Yi Tir Da Matakin Amurka Na Hawa Kujerar Na Ki Game Da Burin Tsagaita Wuta A Gaza

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Gaza

Tun bayan da kasar Amurka ta sake hawa kujerar na ki game da kudurin da aka gabatar a zauren kwamitin tsaron MDD, don gane da gaggauta tsagaita wuta a Gaza a kwanan baya, masharhanta ke ta sukar wannan mataki na Amurka, wanda ko shakka babu ya kara ingiza alummar Gaza cikin karin tashin hankali da yanayi na rashin tabbas. 

 

Alal hakika, abun takaici ne ganin yadda mambobin kwamitin tsaron MDD har 14 suka nuna amincewa da wannan kuduri, amma Amurka ta yi fatali da wannan matsaya tasu, a wani yanayi mai ban takaici da haifar da koma baya, wanda zai wanzar da tashe-tashen hankula da ake gani a Gaza, sama da watanni 13 da sake barkewar rikicin yankin.

ADVERTISEMENT
  • Akpabio Ya Karɓi Baƙuncin Dattawan Niger Delta, Karanta Abin da Suka Tattauna 
  • Gwamna Yusuf Ya Mika Motocin Bas Na CNG Guda 10 Ga Kungiyar NLC Reshen Kano

Idan mun waiwayi baya, za mu ga cewa Amurka ta hau kujerar na ki game da wani kudurin makamancin wannan a ranar 18 ga watan Oktoban bara, lokacin da tuni adadin fararen hula da suka rasu sakamakon rikicin Gaza ya kai kusan mutum 3,000. A karo na biyu da Amurka ta dauki wannan mataki, adadin fararen hular da hare-haren Israila ya hallaka a Gaza ya kai mutum 17,000. Haka dai Amurka ta ci gaba da daukar wannan mataki na hawa kujerar na ki game da kudurin gaggauta kawo karshen wannan rikici, har zuwa karo na 5, inda a ranar 18 ga watan Afrilun bana ta kara hawa kujerar na ki, a gabar da tuni adadin alummun Gaza da suka rasu sanadin wannan rikici suka karu zuwa mutum 34,000.

 

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

A halin da ake ciki yanzu kuwa, wannan adadi ya kai kusan mutum 44,000, amma Amurka ba ta sauya matsaya ba. Hakika wannan lamari ne mai matukar bakanta ran duk wani mai hankali da kaunar zaman lafiya. Adadin mutum 44,000 ba dan kadan ba ne, ya kuma kunshi yara kanana, da mata masu renon jarirai, da masu daukar nauyin bukatun iyalai cikin magidanta, wadanda asarar ran ko wane daya daga cikinsu, ke haifar da tashin hankali da damuwa ta tsawon rayuwa ga zuriyarsa.

 

Don haka, na kan tambayi kai na, shin anya rayuwar Falasdinawa na da wata daraja a idanun gwamnatin Amurka kuwa? Ko Amurka na iya waiwayar wadannan alummu da idon rahama da tausayawa? Abun da na yi imani da shi, shi ne ko bayan kawo karshen wannan tashin hankali, tabbas tarihi zai ci gaba da tunawa da mummunar matsayar Amurka game da matakan nan da take dauka a yanzu, tare da yin tir da halin ko in kula da rayukan dubban Falasdinawa mazauna zirin Gaza. (Saminu Alhassan)

Gaza
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Gaza
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

MASU ALAKA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
Daga Birnin Sin

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
Daga Birnin Sin

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Next Post
Daga Ƙarshe Dai Za A Gudanar da Ƙidayar Ƙasa A 2025

Daga Ƙarshe Dai Za A Gudanar da Ƙidayar Ƙasa A 2025

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.