• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Gusau Da Sarakunanta (1)

by Sulaiman and Idris Aliyu Daudawa
10 months ago
in Tarihi
0
gusau
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Garin Gusau, wani babban birni ne da aka samu bayan Jihadin Sheikh Usman Dan Fodio, wato jihadi na goma sha tara, Mallam Muhammadu Dan Ashafa, shi ne ya samu wannan gari na Gusau a shekarar 1799, a matsayinsa na almajirin Sheikh Danfodio.

Gusau ta fara samun daraja da daukaka ne, bayan koma bayan da aka samu na Yandoto a shekarar 1806. Tun bayan lokacin da ta fara kasancewa mai muhimmanci a Daular Sakkwato, domin kuwa ta ja hankalin al’umma kasancewarta ta wurin yin noma da kuma gudanar da harkokin kasuwanci.

  • Wuraren Tarihi Da Suka Kamata Alhazai Su Ziyarta A Makkah Da Madinah
  • An Gudanar Da Dandalin Kasa Da Kasa Game Da “Tarihi Da Makomar Xinjiang” A Kashgar

Wannan gari na Gusau da kewayensa su yi matukar jan hankalin masana harkar noma da wasu daga cikin manoma da dama. Haka nan, su ma makiyaya; musamman Fulani, wadanda ked a arzikin Shanu. Ana yi wa wannan gari kirari da cewa, Gusau ta Sambo dandin Hausa ko kuma Gusau ta Malam Sambo.

Kafin bayyanar mulkin mallaka, Gusau gari ne na manoma, domin a lokacin noma shi ne babban garin da ake ji da shi ta fannin tattalin arziki, domin noma ne babban ginshikin tattalin arzikin garin, kamar yadda garuruwan Hausa ke sana’ar noma da sauran sana’oi daban-danban da suka hada da sana’ar gini, fawa, kira, maroka da mawaka da sauransu.

Garin Gusau da wasu wuraren da ke makwabtaka da ita, an mika su ga Mallam Sambo Dan Ashafa, wadanda suka kasance a cikin birnin masarautar. A Gusau bayan ta kasance karkashin Mallam Sambon da hedikwatarta take a Gusau; tana da wasu garuruwa da suke karkashin Wonaka, Mada, Yandoto, Samri, Magami, Marabu, Mareri, Mutumji, Kwaren Ganuwa, Wanke da wasu kauyukan da suke zagaye da ita, kamar sauran sassan na Daular Usumaniyya.

Labarai Masu Nasaba

Tarihin Shugaannin Kasar Mali Na Farko A Daular Songhai (8)

Tarihin Shugabannin Ƙasar Mali Na Farko A Daular Songhai (7)

Ta hanyar lamarin tafiyar da mulki, bayan da akwai wadanda suke taimaka wa Gusau din wajen tafiyar da mulkinta, har ila yau sai unguwanni biyar, bayan da aka kasa garin Gusau din zuwa unguwanni ko shiyya kamar yadda sunayensu suke kamar haka, Shiyyar Magaji, Uban Dawaki, Galadima, Mayana da kuma Sarkin Fada. Su ne suke da wata kafa da take sada al’umma tsakaninsu da Dagatai ko masu unguwanni da kuma Sarkin Katsinan Gusau (Emir Of Gusau). Su ne suka kasance kunnuwa da kuma idanun Sarkin. Gusau kamar sauran sassan da ke karkashin Daular Usumaniyya suke, suna aikawa da kason Fadar Sarkin Musulmi na irin kudaden da ta samu.

Bayyanar mulkin mallaka na Turawa ya kawo nau’o’in ci gaban garin na Gusau tare kuma da kungiyoyin da ke cikin birnin. Abubuwan more rayuwa kamar hanyoyi da aka sa wa kwalta, hanyar jirgin kasa, manyan kantuna da wasu harkoki, manyan kamfanoni, duk an kawo su birnin da haka ne kuma Gusau ta kara samun bunkasar ci gaban zamani.

Sai dai, duk da haka wasu tsare-tsaren mulkin mallaka da aka kawo, su ne suka sauya salon mulkin. Idan ba haka ba, garin na Gusau bai kai a rika ba shi wani girma ko daukaka ba, amma sai ga shi cikin kankanin lokaci lamuran sun canza.

Lokacin mulkn mallaka na Turawa, aka fara karbar harajin dabbobi; wato a shekarar 1907, wanda ake kira da (Jangali).

Zamanin mulkin mallakar ne, sana’ar noma ta kasance babbar abin tinkaho wajen bunkasa tattalin arzikin garin na Gusau, hakan kuma sai ya kara bunkasa garin ya kasance na manoma. Sana’ar noma ta zama ba ta da na biyu, idan ana maganar tattalin arziki; wanda ake yi da Damina wajen noma kayan amfanin gona ana ci tare da kuma da sayarwa.

 

Jerin Sunayen Sarakunan Gusau

Malam Sambo Dan Ashafa 1806-1827

Wadannan Sarakuna shida na daga cikin zuri’ar Sambo Dan Ashafa kamar haka:

Malam Abdulkadir 1827-1867

Malam Muhmmadu Modibbo 1867-1876

Malam Muhammad Tuburi 1876-1887

Malam Muhammadu Gide 1887-1900

Malam Muhammadu Murtala 1900-1916

Malam Muhammadu Dangida 1916-1917

Sai dai kuma, daga shekarar 1917 zuwa 1984 ba a bayyana sunayen Sarakunan waccan lokaci ba.

Alhaji Muhammadu Kabir Danbaba, Sarkin Katsinan Gusau 1984-2015

Alhaji Ibrahim Bello 2015 zuwa yanzu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GusauMasarautar SokotoRikicin Masarautar Kano
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zakarun Gasar Olympics 42 Za Su Jagoranci Tawagar Kasar Sin A Gasar Olympics Ta Paris

Next Post

Tinubu Ya Naɗa Baffa Dan Agundi a Matsayin Darakta-Janar

Related

Tarihin Shugaannin Kasar Mali Na Farko A Daular Songhai (8)
Tarihi

Tarihin Shugaannin Kasar Mali Na Farko A Daular Songhai (8)

1 month ago
Tarihin Shugaban Ƙasar Mali Na Farko Sundiata Keita (2)
Tarihi

Tarihin Shugabannin Ƙasar Mali Na Farko A Daular Songhai (7)

1 month ago
A-Ula: Dadadden Birni Mai Cike Da Dinbin Tarihi Da Al’adu
Tarihi

A-Ula: Dadadden Birni Mai Cike Da Dinbin Tarihi Da Al’adu

6 months ago
A Tsame Masarautunmu Daga Siyasa
Al'adu

A Tsame Masarautunmu Daga Siyasa

11 months ago
Gusau
Tarihi

Masarautar Argungu Da Al’adunta (1)

11 months ago
Masarautar Katagum Da Sarakunanta
Tarihi

Masarautar Katagum Da Sarakunanta

12 months ago
Next Post
Tinubu Ya Naɗa Baffa Dan Agundi a Matsayin Darakta-Janar

Tinubu Ya Naɗa Baffa Dan Agundi a Matsayin Darakta-Janar

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.