ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Gusau Da Sarakunanta (1)

by Sulaiman and Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
gusau

Garin Gusau, wani babban birni ne da aka samu bayan Jihadin Sheikh Usman Dan Fodio, wato jihadi na goma sha tara, Mallam Muhammadu Dan Ashafa, shi ne ya samu wannan gari na Gusau a shekarar 1799, a matsayinsa na almajirin Sheikh Danfodio.

Gusau ta fara samun daraja da daukaka ne, bayan koma bayan da aka samu na Yandoto a shekarar 1806. Tun bayan lokacin da ta fara kasancewa mai muhimmanci a Daular Sakkwato, domin kuwa ta ja hankalin al’umma kasancewarta ta wurin yin noma da kuma gudanar da harkokin kasuwanci.

  • Wuraren Tarihi Da Suka Kamata Alhazai Su Ziyarta A Makkah Da Madinah
  • An Gudanar Da Dandalin Kasa Da Kasa Game Da “Tarihi Da Makomar Xinjiang” A Kashgar

Wannan gari na Gusau da kewayensa su yi matukar jan hankalin masana harkar noma da wasu daga cikin manoma da dama. Haka nan, su ma makiyaya; musamman Fulani, wadanda ked a arzikin Shanu. Ana yi wa wannan gari kirari da cewa, Gusau ta Sambo dandin Hausa ko kuma Gusau ta Malam Sambo.

ADVERTISEMENT

Kafin bayyanar mulkin mallaka, Gusau gari ne na manoma, domin a lokacin noma shi ne babban garin da ake ji da shi ta fannin tattalin arziki, domin noma ne babban ginshikin tattalin arzikin garin, kamar yadda garuruwan Hausa ke sana’ar noma da sauran sana’oi daban-danban da suka hada da sana’ar gini, fawa, kira, maroka da mawaka da sauransu.

Garin Gusau da wasu wuraren da ke makwabtaka da ita, an mika su ga Mallam Sambo Dan Ashafa, wadanda suka kasance a cikin birnin masarautar. A Gusau bayan ta kasance karkashin Mallam Sambon da hedikwatarta take a Gusau; tana da wasu garuruwa da suke karkashin Wonaka, Mada, Yandoto, Samri, Magami, Marabu, Mareri, Mutumji, Kwaren Ganuwa, Wanke da wasu kauyukan da suke zagaye da ita, kamar sauran sassan na Daular Usumaniyya.

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)

Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya

Ta hanyar lamarin tafiyar da mulki, bayan da akwai wadanda suke taimaka wa Gusau din wajen tafiyar da mulkinta, har ila yau sai unguwanni biyar, bayan da aka kasa garin Gusau din zuwa unguwanni ko shiyya kamar yadda sunayensu suke kamar haka, Shiyyar Magaji, Uban Dawaki, Galadima, Mayana da kuma Sarkin Fada. Su ne suke da wata kafa da take sada al’umma tsakaninsu da Dagatai ko masu unguwanni da kuma Sarkin Katsinan Gusau (Emir Of Gusau). Su ne suka kasance kunnuwa da kuma idanun Sarkin. Gusau kamar sauran sassan da ke karkashin Daular Usumaniyya suke, suna aikawa da kason Fadar Sarkin Musulmi na irin kudaden da ta samu.

Bayyanar mulkin mallaka na Turawa ya kawo nau’o’in ci gaban garin na Gusau tare kuma da kungiyoyin da ke cikin birnin. Abubuwan more rayuwa kamar hanyoyi da aka sa wa kwalta, hanyar jirgin kasa, manyan kantuna da wasu harkoki, manyan kamfanoni, duk an kawo su birnin da haka ne kuma Gusau ta kara samun bunkasar ci gaban zamani.

Sai dai, duk da haka wasu tsare-tsaren mulkin mallaka da aka kawo, su ne suka sauya salon mulkin. Idan ba haka ba, garin na Gusau bai kai a rika ba shi wani girma ko daukaka ba, amma sai ga shi cikin kankanin lokaci lamuran sun canza.

Lokacin mulkn mallaka na Turawa, aka fara karbar harajin dabbobi; wato a shekarar 1907, wanda ake kira da (Jangali).

Zamanin mulkin mallakar ne, sana’ar noma ta kasance babbar abin tinkaho wajen bunkasa tattalin arzikin garin na Gusau, hakan kuma sai ya kara bunkasa garin ya kasance na manoma. Sana’ar noma ta zama ba ta da na biyu, idan ana maganar tattalin arziki; wanda ake yi da Damina wajen noma kayan amfanin gona ana ci tare da kuma da sayarwa.

 

Jerin Sunayen Sarakunan Gusau

Malam Sambo Dan Ashafa 1806-1827

Wadannan Sarakuna shida na daga cikin zuri’ar Sambo Dan Ashafa kamar haka:

Malam Abdulkadir 1827-1867

Malam Muhmmadu Modibbo 1867-1876

Malam Muhammad Tuburi 1876-1887

Malam Muhammadu Gide 1887-1900

Malam Muhammadu Murtala 1900-1916

Malam Muhammadu Dangida 1916-1917

Sai dai kuma, daga shekarar 1917 zuwa 1984 ba a bayyana sunayen Sarakunan waccan lokaci ba.

Alhaji Muhammadu Kabir Danbaba, Sarkin Katsinan Gusau 1984-2015

Alhaji Ibrahim Bello 2015 zuwa yanzu.

Gusau
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Gusau
Idris Aliyu Daudawa
+ posts Bio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Rayuwar Galadiman Kano Alhaji Tijjani Hashim (2)
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kyamar Baƙi: An Sake Kwaso Ƴan Nijeriya 83 Daga Afirka Ta Kudu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kamfanin Simintin Dangote Ya Tallafa Wa Manoma 60 Da Kayan Aiki A Edo
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tsohon Shugaban Ƙasa Jonathan Ya Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Ƙasa 18 A Jihar Bauchi

MASU ALAKA

Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Tarihi

Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)

May 30, 2026
Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya
Tarihi

Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya

February 22, 2026
Tarihin Sarkin Zazzau Ja’afaru Dan Isiyaku 1936-1959
Tarihi

Tarihin Sarkin Zazzau Ja’afaru Dan Isiyaku 1936-1959. (2)

January 11, 2026
Next Post
Tinubu Ya Naɗa Baffa Dan Agundi a Matsayin Darakta-Janar

Tinubu Ya Naɗa Baffa Dan Agundi a Matsayin Darakta-Janar

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.