ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Gusau Da Sarakunanta (1)

by Sulaiman and Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
gusau

Garin Gusau, wani babban birni ne da aka samu bayan Jihadin Sheikh Usman Dan Fodio, wato jihadi na goma sha tara, Mallam Muhammadu Dan Ashafa, shi ne ya samu wannan gari na Gusau a shekarar 1799, a matsayinsa na almajirin Sheikh Danfodio.

Gusau ta fara samun daraja da daukaka ne, bayan koma bayan da aka samu na Yandoto a shekarar 1806. Tun bayan lokacin da ta fara kasancewa mai muhimmanci a Daular Sakkwato, domin kuwa ta ja hankalin al’umma kasancewarta ta wurin yin noma da kuma gudanar da harkokin kasuwanci.

  • Wuraren Tarihi Da Suka Kamata Alhazai Su Ziyarta A Makkah Da Madinah
  • An Gudanar Da Dandalin Kasa Da Kasa Game Da “Tarihi Da Makomar Xinjiang” A Kashgar

Wannan gari na Gusau da kewayensa su yi matukar jan hankalin masana harkar noma da wasu daga cikin manoma da dama. Haka nan, su ma makiyaya; musamman Fulani, wadanda ked a arzikin Shanu. Ana yi wa wannan gari kirari da cewa, Gusau ta Sambo dandin Hausa ko kuma Gusau ta Malam Sambo.

ADVERTISEMENT

Kafin bayyanar mulkin mallaka, Gusau gari ne na manoma, domin a lokacin noma shi ne babban garin da ake ji da shi ta fannin tattalin arziki, domin noma ne babban ginshikin tattalin arzikin garin, kamar yadda garuruwan Hausa ke sana’ar noma da sauran sana’oi daban-danban da suka hada da sana’ar gini, fawa, kira, maroka da mawaka da sauransu.

Garin Gusau da wasu wuraren da ke makwabtaka da ita, an mika su ga Mallam Sambo Dan Ashafa, wadanda suka kasance a cikin birnin masarautar. A Gusau bayan ta kasance karkashin Mallam Sambon da hedikwatarta take a Gusau; tana da wasu garuruwa da suke karkashin Wonaka, Mada, Yandoto, Samri, Magami, Marabu, Mareri, Mutumji, Kwaren Ganuwa, Wanke da wasu kauyukan da suke zagaye da ita, kamar sauran sassan na Daular Usumaniyya.

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)

Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya

Ta hanyar lamarin tafiyar da mulki, bayan da akwai wadanda suke taimaka wa Gusau din wajen tafiyar da mulkinta, har ila yau sai unguwanni biyar, bayan da aka kasa garin Gusau din zuwa unguwanni ko shiyya kamar yadda sunayensu suke kamar haka, Shiyyar Magaji, Uban Dawaki, Galadima, Mayana da kuma Sarkin Fada. Su ne suke da wata kafa da take sada al’umma tsakaninsu da Dagatai ko masu unguwanni da kuma Sarkin Katsinan Gusau (Emir Of Gusau). Su ne suka kasance kunnuwa da kuma idanun Sarkin. Gusau kamar sauran sassan da ke karkashin Daular Usumaniyya suke, suna aikawa da kason Fadar Sarkin Musulmi na irin kudaden da ta samu.

Bayyanar mulkin mallaka na Turawa ya kawo nau’o’in ci gaban garin na Gusau tare kuma da kungiyoyin da ke cikin birnin. Abubuwan more rayuwa kamar hanyoyi da aka sa wa kwalta, hanyar jirgin kasa, manyan kantuna da wasu harkoki, manyan kamfanoni, duk an kawo su birnin da haka ne kuma Gusau ta kara samun bunkasar ci gaban zamani.

Sai dai, duk da haka wasu tsare-tsaren mulkin mallaka da aka kawo, su ne suka sauya salon mulkin. Idan ba haka ba, garin na Gusau bai kai a rika ba shi wani girma ko daukaka ba, amma sai ga shi cikin kankanin lokaci lamuran sun canza.

Lokacin mulkn mallaka na Turawa, aka fara karbar harajin dabbobi; wato a shekarar 1907, wanda ake kira da (Jangali).

Zamanin mulkin mallakar ne, sana’ar noma ta kasance babbar abin tinkaho wajen bunkasa tattalin arzikin garin na Gusau, hakan kuma sai ya kara bunkasa garin ya kasance na manoma. Sana’ar noma ta zama ba ta da na biyu, idan ana maganar tattalin arziki; wanda ake yi da Damina wajen noma kayan amfanin gona ana ci tare da kuma da sayarwa.

 

Jerin Sunayen Sarakunan Gusau

Malam Sambo Dan Ashafa 1806-1827

Wadannan Sarakuna shida na daga cikin zuri’ar Sambo Dan Ashafa kamar haka:

Malam Abdulkadir 1827-1867

Malam Muhmmadu Modibbo 1867-1876

Malam Muhammad Tuburi 1876-1887

Malam Muhammadu Gide 1887-1900

Malam Muhammadu Murtala 1900-1916

Malam Muhammadu Dangida 1916-1917

Sai dai kuma, daga shekarar 1917 zuwa 1984 ba a bayyana sunayen Sarakunan waccan lokaci ba.

Alhaji Muhammadu Kabir Danbaba, Sarkin Katsinan Gusau 1984-2015

Alhaji Ibrahim Bello 2015 zuwa yanzu.

Gusau
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
  • Sulaiman
    Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba
  • Sulaiman
    Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Gusau
Idris Aliyu Daudawa
+ posts Bio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

MASU ALAKA

Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Tarihi

Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)

May 30, 2026
Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya
Tarihi

Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya

February 22, 2026
Tarihin Sarkin Zazzau Ja’afaru Dan Isiyaku 1936-1959
Tarihi

Tarihin Sarkin Zazzau Ja’afaru Dan Isiyaku 1936-1959. (2)

January 11, 2026
Next Post
Tinubu Ya Naɗa Baffa Dan Agundi a Matsayin Darakta-Janar

Tinubu Ya Naɗa Baffa Dan Agundi a Matsayin Darakta-Janar

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.