ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Gusau Da Sarakunanta (1)

by Sulaiman and Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
gusau

Garin Gusau, wani babban birni ne da aka samu bayan Jihadin Sheikh Usman Dan Fodio, wato jihadi na goma sha tara, Mallam Muhammadu Dan Ashafa, shi ne ya samu wannan gari na Gusau a shekarar 1799, a matsayinsa na almajirin Sheikh Danfodio.

Gusau ta fara samun daraja da daukaka ne, bayan koma bayan da aka samu na Yandoto a shekarar 1806. Tun bayan lokacin da ta fara kasancewa mai muhimmanci a Daular Sakkwato, domin kuwa ta ja hankalin al’umma kasancewarta ta wurin yin noma da kuma gudanar da harkokin kasuwanci.

  • Wuraren Tarihi Da Suka Kamata Alhazai Su Ziyarta A Makkah Da Madinah
  • An Gudanar Da Dandalin Kasa Da Kasa Game Da “Tarihi Da Makomar Xinjiang” A Kashgar

Wannan gari na Gusau da kewayensa su yi matukar jan hankalin masana harkar noma da wasu daga cikin manoma da dama. Haka nan, su ma makiyaya; musamman Fulani, wadanda ked a arzikin Shanu. Ana yi wa wannan gari kirari da cewa, Gusau ta Sambo dandin Hausa ko kuma Gusau ta Malam Sambo.

ADVERTISEMENT

Kafin bayyanar mulkin mallaka, Gusau gari ne na manoma, domin a lokacin noma shi ne babban garin da ake ji da shi ta fannin tattalin arziki, domin noma ne babban ginshikin tattalin arzikin garin, kamar yadda garuruwan Hausa ke sana’ar noma da sauran sana’oi daban-danban da suka hada da sana’ar gini, fawa, kira, maroka da mawaka da sauransu.

Garin Gusau da wasu wuraren da ke makwabtaka da ita, an mika su ga Mallam Sambo Dan Ashafa, wadanda suka kasance a cikin birnin masarautar. A Gusau bayan ta kasance karkashin Mallam Sambon da hedikwatarta take a Gusau; tana da wasu garuruwa da suke karkashin Wonaka, Mada, Yandoto, Samri, Magami, Marabu, Mareri, Mutumji, Kwaren Ganuwa, Wanke da wasu kauyukan da suke zagaye da ita, kamar sauran sassan na Daular Usumaniyya.

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)

Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya

Ta hanyar lamarin tafiyar da mulki, bayan da akwai wadanda suke taimaka wa Gusau din wajen tafiyar da mulkinta, har ila yau sai unguwanni biyar, bayan da aka kasa garin Gusau din zuwa unguwanni ko shiyya kamar yadda sunayensu suke kamar haka, Shiyyar Magaji, Uban Dawaki, Galadima, Mayana da kuma Sarkin Fada. Su ne suke da wata kafa da take sada al’umma tsakaninsu da Dagatai ko masu unguwanni da kuma Sarkin Katsinan Gusau (Emir Of Gusau). Su ne suka kasance kunnuwa da kuma idanun Sarkin. Gusau kamar sauran sassan da ke karkashin Daular Usumaniyya suke, suna aikawa da kason Fadar Sarkin Musulmi na irin kudaden da ta samu.

Bayyanar mulkin mallaka na Turawa ya kawo nau’o’in ci gaban garin na Gusau tare kuma da kungiyoyin da ke cikin birnin. Abubuwan more rayuwa kamar hanyoyi da aka sa wa kwalta, hanyar jirgin kasa, manyan kantuna da wasu harkoki, manyan kamfanoni, duk an kawo su birnin da haka ne kuma Gusau ta kara samun bunkasar ci gaban zamani.

Sai dai, duk da haka wasu tsare-tsaren mulkin mallaka da aka kawo, su ne suka sauya salon mulkin. Idan ba haka ba, garin na Gusau bai kai a rika ba shi wani girma ko daukaka ba, amma sai ga shi cikin kankanin lokaci lamuran sun canza.

Lokacin mulkn mallaka na Turawa, aka fara karbar harajin dabbobi; wato a shekarar 1907, wanda ake kira da (Jangali).

Zamanin mulkin mallakar ne, sana’ar noma ta kasance babbar abin tinkaho wajen bunkasa tattalin arzikin garin na Gusau, hakan kuma sai ya kara bunkasa garin ya kasance na manoma. Sana’ar noma ta zama ba ta da na biyu, idan ana maganar tattalin arziki; wanda ake yi da Damina wajen noma kayan amfanin gona ana ci tare da kuma da sayarwa.

 

Jerin Sunayen Sarakunan Gusau

Malam Sambo Dan Ashafa 1806-1827

Wadannan Sarakuna shida na daga cikin zuri’ar Sambo Dan Ashafa kamar haka:

Malam Abdulkadir 1827-1867

Malam Muhmmadu Modibbo 1867-1876

Malam Muhammad Tuburi 1876-1887

Malam Muhammadu Gide 1887-1900

Malam Muhammadu Murtala 1900-1916

Malam Muhammadu Dangida 1916-1917

Sai dai kuma, daga shekarar 1917 zuwa 1984 ba a bayyana sunayen Sarakunan waccan lokaci ba.

Alhaji Muhammadu Kabir Danbaba, Sarkin Katsinan Gusau 1984-2015

Alhaji Ibrahim Bello 2015 zuwa yanzu.

Gusau
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Gusau
Idris Aliyu Daudawa
+ posts Bio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar NCCE Ta Yi Tsare-tsaren Bunƙasa Horar Da Malamai
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Abubuwan Da Ya Kamata Magidanci Ya Sani Bayan Matarsa Ta Haihu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir

MASU ALAKA

Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Tarihi

Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)

May 30, 2026
Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya
Tarihi

Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya

February 22, 2026
Tarihin Sarkin Zazzau Ja’afaru Dan Isiyaku 1936-1959
Tarihi

Tarihin Sarkin Zazzau Ja’afaru Dan Isiyaku 1936-1959. (2)

January 11, 2026
Next Post
Tinubu Ya Naɗa Baffa Dan Agundi a Matsayin Darakta-Janar

Tinubu Ya Naɗa Baffa Dan Agundi a Matsayin Darakta-Janar

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.