• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Hadejia Da Sarakunanta (4)

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
Zakka

….Ci gaba daga makon da ya gabata

A wannan makon za mu duba Sarki na 6 a jerin wadanda suka muki masarautar Hadejia.

6. Buhari bin Sambo, 1848-50 zuwa 1851-1863
Abubakar Buhari bin Muhammad Sambo Digimsa shine Sarkin Hadejia na 4 amma bayan shekaru na Jihadi,ya kuma kasance a zamanin mulkinsa ne lokacin da ba za a manta da shi bane musamman ma idan ana maganar tarihin Hadejia.Sambo ya mutu ne a shekarar 1848 kuma sai ta kasance a hannun Buhari, kafin rasuwar mahaifinsa sai abin ya kasance duk wani salon iya mulki an nuna ma sa su maimakon a nuna wa Ahamadu wanda shi Sambo yana ganin shi ne zai gaje shi bayan rasuwarsa.

Duk da yake Buhari ne ya zama Sarkin Hadejia a wata matsalar da aka samu amma amincewa da hawan gadon Sarautar shi daga Sakkwato ne aka samu amincewar hakan.Buhari bai dade da hawa gadon Sarauta ba sai aka kashe dan’uwansa, Nalara Sarkin Auyo,wanda wani al’amari ne da yaba mahukuntan Sakkwato wata dama da suke jira ta cire ta cire Buhari daga gadon Sarauta.

Hakanan ma a shekarar 1850 da yake ba a samu nasarar ta hanyar difilomasiyya ba sai Kalifanci ya ba Wazirin Sakkwato umarni tare da taimakon wasu dakaru daga Katagum domin a dora dan’uwan Buhari Ahmadu a matsayin sabon Sarkin masarautar Hadejia za ayi hakan ne amma idan an samu wata dama.

LABARAI MASU NASABA

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

Tarihin ‘Yan Majalisar Farko A Nijeriya Kafin Zamanin Mulkin Mallaka

Daga karshe dai an nada Ahamadu a matsayin Sarkin Hadejia a shekarar 1850 sai kuma Buhari ya koma Machina wato irin al’amarin nan da idan aka fidda Sarkin daga Sarauta ba’a barinsa a garin sai a kai shi wani wuri kamar yadda aka yi ma marigayi Sarkin Kano Muhammadu Sanusi na 1, zamanin jamhuriya ta farko aka kai shi Katagum shekaar 1950 lokacin da aka nada Ado Bayero matsayin sabon Sarkin Kano.Sai dai kuma wani al’amari na Allah cikin shekara daya ce kawai sai ga Buhari ya sake dawowa Hadejia inda ya fafata a shekarar 1851,bayan samun dakaru masu yawa da kuma kayan aiki wato Kudi ya fuskanci dakarun dan ‘uwansa Ahamadu duk kuwa da yake ya samu taimako daga Katagum, sai ga shi an samu galaba a kan dakarun shi aka kashe Ahamadu a fagen daga ba tare da wata wahala ba.Ta haka ne Buhari ya sake dawowa mulkin Hadejia a matsayin Sarkin ta duk da yake mahukunta na Sakkwato basu so,wannan shi ne mafarin maganar nan da ake yi mata lakabi da adawar Buhari ko abin nan da aka cewa (Taskar Suleiman Ginsau).

Sarkin Hadejia ya yi shekaru goma sha biyar yana matsayin kamar dan tawaye saboda ya cire masarautar Hadejia daga daular Usumaniyya da hedikwatarta ke Sakkwato.Abu daya da yake babbane shine yadda rashin biyayya ko goyon bayan Buhari ga daular Usumaniyya abin ya kara fitowa fili ne a wani artabu da aka yi a kauyen Kaffur.

 

A shekarar 1853 ce daular Usumaniyya ta sake daukatr wani mataki wanda take ganin zai iya kawo karshen wani Kallon masheka Ayar da ya ke yi mata, domin duk wadansu masarautun da ake yi ma kalon suna da kima an sa su a cikin yakin,amma daga karshe duk sai kidin nasu ya kare a jinjina.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

September 5, 2025
majalisar kasa
Tarihi

Tarihin ‘Yan Majalisar Farko A Nijeriya Kafin Zamanin Mulkin Mallaka

August 30, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)
Tarihi

Dalilan Da Suka Sa Cinikin Bayi Bai Yi Nasara A Arewacin Nijeriya Ba

July 26, 2025
Next Post
Thailand

Firaministan Thailand: Cudanya Da Juna Bisa Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Raya Ci Gaban Shiyyoyi

LABARAI MASU NASABA

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

October 9, 2025
SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.