ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Hadejia Da Sarakunanta (4)

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
Zakka

….Ci gaba daga makon da ya gabata

A wannan makon za mu duba Sarki na 6 a jerin wadanda suka muki masarautar Hadejia.

6. Buhari bin Sambo, 1848-50 zuwa 1851-1863
Abubakar Buhari bin Muhammad Sambo Digimsa shine Sarkin Hadejia na 4 amma bayan shekaru na Jihadi,ya kuma kasance a zamanin mulkinsa ne lokacin da ba za a manta da shi bane musamman ma idan ana maganar tarihin Hadejia.Sambo ya mutu ne a shekarar 1848 kuma sai ta kasance a hannun Buhari, kafin rasuwar mahaifinsa sai abin ya kasance duk wani salon iya mulki an nuna ma sa su maimakon a nuna wa Ahamadu wanda shi Sambo yana ganin shi ne zai gaje shi bayan rasuwarsa.

ADVERTISEMENT

Duk da yake Buhari ne ya zama Sarkin Hadejia a wata matsalar da aka samu amma amincewa da hawan gadon Sarautar shi daga Sakkwato ne aka samu amincewar hakan.Buhari bai dade da hawa gadon Sarauta ba sai aka kashe dan’uwansa, Nalara Sarkin Auyo,wanda wani al’amari ne da yaba mahukuntan Sakkwato wata dama da suke jira ta cire ta cire Buhari daga gadon Sarauta.

Hakanan ma a shekarar 1850 da yake ba a samu nasarar ta hanyar difilomasiyya ba sai Kalifanci ya ba Wazirin Sakkwato umarni tare da taimakon wasu dakaru daga Katagum domin a dora dan’uwan Buhari Ahmadu a matsayin sabon Sarkin masarautar Hadejia za ayi hakan ne amma idan an samu wata dama.

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)

Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya

Daga karshe dai an nada Ahamadu a matsayin Sarkin Hadejia a shekarar 1850 sai kuma Buhari ya koma Machina wato irin al’amarin nan da idan aka fidda Sarkin daga Sarauta ba’a barinsa a garin sai a kai shi wani wuri kamar yadda aka yi ma marigayi Sarkin Kano Muhammadu Sanusi na 1, zamanin jamhuriya ta farko aka kai shi Katagum shekaar 1950 lokacin da aka nada Ado Bayero matsayin sabon Sarkin Kano.Sai dai kuma wani al’amari na Allah cikin shekara daya ce kawai sai ga Buhari ya sake dawowa Hadejia inda ya fafata a shekarar 1851,bayan samun dakaru masu yawa da kuma kayan aiki wato Kudi ya fuskanci dakarun dan ‘uwansa Ahamadu duk kuwa da yake ya samu taimako daga Katagum, sai ga shi an samu galaba a kan dakarun shi aka kashe Ahamadu a fagen daga ba tare da wata wahala ba.Ta haka ne Buhari ya sake dawowa mulkin Hadejia a matsayin Sarkin ta duk da yake mahukunta na Sakkwato basu so,wannan shi ne mafarin maganar nan da ake yi mata lakabi da adawar Buhari ko abin nan da aka cewa (Taskar Suleiman Ginsau).

Sarkin Hadejia ya yi shekaru goma sha biyar yana matsayin kamar dan tawaye saboda ya cire masarautar Hadejia daga daular Usumaniyya da hedikwatarta ke Sakkwato.Abu daya da yake babbane shine yadda rashin biyayya ko goyon bayan Buhari ga daular Usumaniyya abin ya kara fitowa fili ne a wani artabu da aka yi a kauyen Kaffur.

 

A shekarar 1853 ce daular Usumaniyya ta sake daukatr wani mataki wanda take ganin zai iya kawo karshen wani Kallon masheka Ayar da ya ke yi mata, domin duk wadansu masarautun da ake yi ma kalon suna da kima an sa su a cikin yakin,amma daga karshe duk sai kidin nasu ya kare a jinjina.

Hadejia
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

MASU ALAKA

Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Tarihi

Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)

May 30, 2026
Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya
Tarihi

Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya

February 22, 2026
Tarihin Sarkin Zazzau Ja’afaru Dan Isiyaku 1936-1959
Tarihi

Tarihin Sarkin Zazzau Ja’afaru Dan Isiyaku 1936-1959. (2)

January 11, 2026
Next Post
Thailand

Firaministan Thailand: Cudanya Da Juna Bisa Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Na Raya Ci Gaban Shiyyoyi

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.