• English
  • Business News
Friday, May 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Hadejia Da Sarakunanta (6)

Ci gaba daga makon da ya gabata

by Idris Aliyu Daudawa
1 year ago
in Tarihi
0
Tarihin Hadejia Da Sarakunanta (6)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Tarihin Shugaannin Kasar Mali Na Farko A Daular Songhai (8)

Tarihin Shugabannin Ƙasar Mali Na Farko A Daular Songhai (7)

8.Umaru bin Buhari,1863-1865

Bayan rasuwar Buhari a fagen daga ko yaki sai dansa Umaru ya zama Sarkin Hadejia na bakwai lokacin ya na da shekara 18.Ya samu damar hawan karagar mulkin ne ta taimakon Sarkin Arewa Tatagana da Sarkin yakin Hadejia Jaji, wanda shi ne mai fada aji kuma bawa na Buhari. (Taskar Suleiman Ginsau).Daular Usumaniyya ce ta amince da nada shi Sarkin a wani kokarin da ta ke  yi na maido da Hadejia karkashin daular Usumaniyya. Sai dai kuma Sarkin Hadejia Umaru ya yi sarauta ne ta shekara biyu, wani abu daban shekarun na da matukar muhimmanci.Kawunsa Haru yana sha’awar zama Sarkin Hadejia, saboda kuwa  a asirce yana kokarin yadda zai raba Umaru da ci gaba da kasancewa ko zama a matsayin Sarkin ta.Da farko sai da aka fara gamawa da Tatagana da  Jiji,wadanda sune suka fi kowa nuna goyon baya ga Umaru a wani shirin da ake yi na raba shi da sarautar.Da haka ne lokacin da Sarkin Hadejia   Umaru ya fita a tafiyar da ya kan yi ta zuwa Kogin Hadejia abin da ya faru shine sai wasu taga cikin ‘yan tawagar shi suka bar shi , suka kkuma hana shi komawa birnin Hadejia.Daga nan sai Sarkin Hadejia Umaru ya yi murabus zuwa Chamo karkashin masarautar Kano inda ya zauna har karshen rayuwarsa ya mutu a shekara 1920. (Taskar Suleiman Ginsau)

  1. Haru bin Sambo, 1865-1885

Da aka yi nasarar cire Umaru daga Sarautar Hadejia sai Haru (Babba )ya haye kan karagar mulki a matsayin Sarkin Hadejia ya yi shekara 20 yana mulki inda ya kawo sauye- sauye a masarautar Hadejia,ya kara bunkasa Ganuwar zuwa yadda take a halin yanzu.Ya gabatar da mulkinsa inda ya kara daukaka tafarkin addinin musulunci ta hanyar bude makarantun Islamiyya da kuma kiran Malamai wadanda suka san al’amarin musulunci daga sauran masarautu. Bai tsaya a nan ba domin kuwa an samu labarin cewar yana  masana addinin musulunci akan hanyarsu ta zuwa Makka inda yake basu shawarar su zauna a Hadejia saboda sha’awar da yake da ita ta yada addinin musulunci.

Bugu da kari lokacin shi ne aka kara fadadad Masallacin Jumma’ar birnin Hadejia inda  ya kara kasancewa babba.Ta bangaren zamantakewa da bunkasa tattalin arzikin ya tsarin ya ya jawo hankalin ‘yankasuwar kasshen  waje zuwa kasuwannin Hadejia. Ya yi hakan ne ta rage harajin shigowa da wasu kaya.Bayan nan kuma ya yaki wadanda ba musulmi ba wasu wuraren  Kare-Kare da Bade,wannan shi ya yi sanadiyar hada Adiani zuwa masarautar  Hadejia.Hakanan ma  a zamanin  sarautar Haru ne aka kawo karshen yawan zaman Manja da Doya da ake yi tsakanin Hadejia da Gumel  inda aka yi babban yaki a Zaburam  shekarar 1872, a lokacin ne aka kashe Sarkin Gumel  Abdu Jatau. Wannan nasarar ce ta kawo karshen yawan yake- yaken da ake yi tsakanin Hadejia da Gumel. Sakin Hadejia Haru ya mutu a shekarar 1885.(Taskar Suleiman Ginsau)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tattaunawa Game Da Wankan Jego (2)

Next Post

An Gano Wasu Mutum 14 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Kaduna

Related

Tarihin Shugaannin Kasar Mali Na Farko A Daular Songhai (8)
Tarihi

Tarihin Shugaannin Kasar Mali Na Farko A Daular Songhai (8)

1 month ago
Tarihin Shugaban Ƙasar Mali Na Farko Sundiata Keita (2)
Tarihi

Tarihin Shugabannin Ƙasar Mali Na Farko A Daular Songhai (7)

2 months ago
A-Ula: Dadadden Birni Mai Cike Da Dinbin Tarihi Da Al’adu
Tarihi

A-Ula: Dadadden Birni Mai Cike Da Dinbin Tarihi Da Al’adu

7 months ago
gusau
Tarihi

Tarihin Gusau Da Sarakunanta (1)

10 months ago
A Tsame Masarautunmu Daga Siyasa
Al'adu

A Tsame Masarautunmu Daga Siyasa

11 months ago
Hadejia
Tarihi

Masarautar Argungu Da Al’adunta (1)

12 months ago
Next Post
Wani Abun Fashewa Ya Tarwatse A Wata Islamiyya, Ɗalibi 1 Ya Rasu, 10 Sun Jikkata A Kaduna

An Gano Wasu Mutum 14 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

Kasar Sin Ta Yanke Shawarar Hana Taiwan Halartar Babban Taron WHO Na Bana

May 15, 2025
Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA

May 15, 2025
Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

Sin Ta Bukaci Amurka Ta Dakatar Da Harajin Sashe Na 232

May 15, 2025
Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

Xi Ya Taya Shugaban Togo Murnar Karbar Ragamar Shugabanci

May 15, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisar Wakilai Za Ta Binciki Yadda Aka Samu Mummunan Sakamakon Jarabawar UTME 2025

May 15, 2025
Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Yi Karin Haske Kan Huldar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

May 15, 2025
An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

May 15, 2025
HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

May 15, 2025
Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

May 15, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.