• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Hadejia Da Sarakunanta (6)

Ci gaba daga makon da ya gabata

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
in Tarihi
0
Tarihin Hadejia Da Sarakunanta (6)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

Tarihin ‘Yan Majalisar Farko A Nijeriya Kafin Zamanin Mulkin Mallaka

8.Umaru bin Buhari,1863-1865

Bayan rasuwar Buhari a fagen daga ko yaki sai dansa Umaru ya zama Sarkin Hadejia na bakwai lokacin ya na da shekara 18.Ya samu damar hawan karagar mulkin ne ta taimakon Sarkin Arewa Tatagana da Sarkin yakin Hadejia Jaji, wanda shi ne mai fada aji kuma bawa na Buhari. (Taskar Suleiman Ginsau).Daular Usumaniyya ce ta amince da nada shi Sarkin a wani kokarin da ta ke  yi na maido da Hadejia karkashin daular Usumaniyya. Sai dai kuma Sarkin Hadejia Umaru ya yi sarauta ne ta shekara biyu, wani abu daban shekarun na da matukar muhimmanci.Kawunsa Haru yana sha’awar zama Sarkin Hadejia, saboda kuwa  a asirce yana kokarin yadda zai raba Umaru da ci gaba da kasancewa ko zama a matsayin Sarkin ta.Da farko sai da aka fara gamawa da Tatagana da  Jiji,wadanda sune suka fi kowa nuna goyon baya ga Umaru a wani shirin da ake yi na raba shi da sarautar.Da haka ne lokacin da Sarkin Hadejia   Umaru ya fita a tafiyar da ya kan yi ta zuwa Kogin Hadejia abin da ya faru shine sai wasu taga cikin ‘yan tawagar shi suka bar shi , suka kkuma hana shi komawa birnin Hadejia.Daga nan sai Sarkin Hadejia Umaru ya yi murabus zuwa Chamo karkashin masarautar Kano inda ya zauna har karshen rayuwarsa ya mutu a shekara 1920. (Taskar Suleiman Ginsau)

  1. Haru bin Sambo, 1865-1885

Da aka yi nasarar cire Umaru daga Sarautar Hadejia sai Haru (Babba )ya haye kan karagar mulki a matsayin Sarkin Hadejia ya yi shekara 20 yana mulki inda ya kawo sauye- sauye a masarautar Hadejia,ya kara bunkasa Ganuwar zuwa yadda take a halin yanzu.Ya gabatar da mulkinsa inda ya kara daukaka tafarkin addinin musulunci ta hanyar bude makarantun Islamiyya da kuma kiran Malamai wadanda suka san al’amarin musulunci daga sauran masarautu. Bai tsaya a nan ba domin kuwa an samu labarin cewar yana  masana addinin musulunci akan hanyarsu ta zuwa Makka inda yake basu shawarar su zauna a Hadejia saboda sha’awar da yake da ita ta yada addinin musulunci.

Bugu da kari lokacin shi ne aka kara fadadad Masallacin Jumma’ar birnin Hadejia inda  ya kara kasancewa babba.Ta bangaren zamantakewa da bunkasa tattalin arzikin ya tsarin ya ya jawo hankalin ‘yankasuwar kasshen  waje zuwa kasuwannin Hadejia. Ya yi hakan ne ta rage harajin shigowa da wasu kaya.Bayan nan kuma ya yaki wadanda ba musulmi ba wasu wuraren  Kare-Kare da Bade,wannan shi ya yi sanadiyar hada Adiani zuwa masarautar  Hadejia.Hakanan ma  a zamanin  sarautar Haru ne aka kawo karshen yawan zaman Manja da Doya da ake yi tsakanin Hadejia da Gumel  inda aka yi babban yaki a Zaburam  shekarar 1872, a lokacin ne aka kashe Sarkin Gumel  Abdu Jatau. Wannan nasarar ce ta kawo karshen yawan yake- yaken da ake yi tsakanin Hadejia da Gumel. Sakin Hadejia Haru ya mutu a shekarar 1885.(Taskar Suleiman Ginsau)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tattaunawa Game Da Wankan Jego (2)

Next Post

An Gano Wasu Mutum 14 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Kaduna

Related

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da É—umi-É—uminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

2 weeks ago
majalisar kasa
Tarihi

Tarihin ‘Yan Majalisar Farko A Nijeriya Kafin Zamanin Mulkin Mallaka

3 weeks ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)
Tarihi

Dalilan Da Suka Sa Cinikin Bayi Bai Yi Nasara A Arewacin Nijeriya Ba

2 months ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)
Tarihi

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)

2 months ago
Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)
Tarihi

Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)

3 months ago
Tarihin Shugaannin Kasar Mali Na Farko A Daular Songhai (8)
Tarihi

Tarihin Shugaannin Kasar Mali Na Farko A Daular Songhai (8)

6 months ago
Next Post
Wani Abun Fashewa Ya Tarwatse A Wata Islamiyya, ÆŠalibi 1 Ya Rasu, 10 Sun Jikkata A Kaduna

An Gano Wasu Mutum 14 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

Shugaba Xi ya zanta ta wayar tarho da takwaransa na Amurka

September 19, 2025
Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

September 19, 2025
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

September 19, 2025
Hadejia

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

September 19, 2025
Xi Jinping Ya Aika Wasikar Taya Murnar Cika Shekaru 100 Da Kafuwar Jam’iyyar Zhigong Ta Sin

Xi Jinping Ya Aika Wasikar Taya Murnar Cika Shekaru 100 Da Kafuwar Jam’iyyar Zhigong Ta Sin

September 19, 2025
An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

September 19, 2025
Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

September 19, 2025
Hadejia

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.