• English
  • Business News
Saturday, October 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Hadejia Da Sarakunanta (6)

Ci gaba daga makon da ya gabata

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
Hadejia

LABARAI MASU NASABA

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

Tarihin ‘Yan Majalisar Farko A Nijeriya Kafin Zamanin Mulkin Mallaka

8.Umaru bin Buhari,1863-1865

Bayan rasuwar Buhari a fagen daga ko yaki sai dansa Umaru ya zama Sarkin Hadejia na bakwai lokacin ya na da shekara 18.Ya samu damar hawan karagar mulkin ne ta taimakon Sarkin Arewa Tatagana da Sarkin yakin Hadejia Jaji, wanda shi ne mai fada aji kuma bawa na Buhari. (Taskar Suleiman Ginsau).Daular Usumaniyya ce ta amince da nada shi Sarkin a wani kokarin da ta ke  yi na maido da Hadejia karkashin daular Usumaniyya. Sai dai kuma Sarkin Hadejia Umaru ya yi sarauta ne ta shekara biyu, wani abu daban shekarun na da matukar muhimmanci.Kawunsa Haru yana sha’awar zama Sarkin Hadejia, saboda kuwa  a asirce yana kokarin yadda zai raba Umaru da ci gaba da kasancewa ko zama a matsayin Sarkin ta.Da farko sai da aka fara gamawa da Tatagana da  Jiji,wadanda sune suka fi kowa nuna goyon baya ga Umaru a wani shirin da ake yi na raba shi da sarautar.Da haka ne lokacin da Sarkin Hadejia   Umaru ya fita a tafiyar da ya kan yi ta zuwa Kogin Hadejia abin da ya faru shine sai wasu taga cikin ‘yan tawagar shi suka bar shi , suka kkuma hana shi komawa birnin Hadejia.Daga nan sai Sarkin Hadejia Umaru ya yi murabus zuwa Chamo karkashin masarautar Kano inda ya zauna har karshen rayuwarsa ya mutu a shekara 1920. (Taskar Suleiman Ginsau)

  1. Haru bin Sambo, 1865-1885

Da aka yi nasarar cire Umaru daga Sarautar Hadejia sai Haru (Babba )ya haye kan karagar mulki a matsayin Sarkin Hadejia ya yi shekara 20 yana mulki inda ya kawo sauye- sauye a masarautar Hadejia,ya kara bunkasa Ganuwar zuwa yadda take a halin yanzu.Ya gabatar da mulkinsa inda ya kara daukaka tafarkin addinin musulunci ta hanyar bude makarantun Islamiyya da kuma kiran Malamai wadanda suka san al’amarin musulunci daga sauran masarautu. Bai tsaya a nan ba domin kuwa an samu labarin cewar yana  masana addinin musulunci akan hanyarsu ta zuwa Makka inda yake basu shawarar su zauna a Hadejia saboda sha’awar da yake da ita ta yada addinin musulunci.

Bugu da kari lokacin shi ne aka kara fadadad Masallacin Jumma’ar birnin Hadejia inda  ya kara kasancewa babba.Ta bangaren zamantakewa da bunkasa tattalin arzikin ya tsarin ya ya jawo hankalin ‘yankasuwar kasshen  waje zuwa kasuwannin Hadejia. Ya yi hakan ne ta rage harajin shigowa da wasu kaya.Bayan nan kuma ya yaki wadanda ba musulmi ba wasu wuraren  Kare-Kare da Bade,wannan shi ya yi sanadiyar hada Adiani zuwa masarautar  Hadejia.Hakanan ma  a zamanin  sarautar Haru ne aka kawo karshen yawan zaman Manja da Doya da ake yi tsakanin Hadejia da Gumel  inda aka yi babban yaki a Zaburam  shekarar 1872, a lokacin ne aka kashe Sarkin Gumel  Abdu Jatau. Wannan nasarar ce ta kawo karshen yawan yake- yaken da ake yi tsakanin Hadejia da Gumel. Sakin Hadejia Haru ya mutu a shekarar 1885.(Taskar Suleiman Ginsau)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

September 5, 2025
majalisar kasa
Tarihi

Tarihin ‘Yan Majalisar Farko A Nijeriya Kafin Zamanin Mulkin Mallaka

August 30, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)
Tarihi

Dalilan Da Suka Sa Cinikin Bayi Bai Yi Nasara A Arewacin Nijeriya Ba

July 26, 2025
Next Post
Wani Abun Fashewa Ya Tarwatse A Wata Islamiyya, Ɗalibi 1 Ya Rasu, 10 Sun Jikkata A Kaduna

An Gano Wasu Mutum 14 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Matashi Ya Kashe Ɗan Acaɓa Don Neman Kuɗin Auren Mace Ta Uku A Bauchi

October 17, 2025
katsina

Tawagar Bankin Duniya Ta Gana Da Gwamnan Katsina Kan Mayar Da ‘Yan Gudun Hijira Muhallinsu

October 17, 2025
Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

October 17, 2025
Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

Akwai Bukatar Al’umma Ta San Aikin Da Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFUND) Ya Yi  – Masari

October 17, 2025
Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

Ma’aikatar Cinikayyar Kasar Sin Ta Fitar Da Rahoton Shekarar 2025 Game Da Biyayyar Amurka Ga Ka’idojin WTO

October 17, 2025
Abduljabbar

Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja

October 17, 2025
An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

An Kara Habaka Sabon Karfin Samar Da Kayayyaki Da Hidimomi Mai Dorewa a Cikin Watannin Tara Na Farkon Bana

October 17, 2025
Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki

Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki

October 17, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Gwamnatin Kano Ta Kai Ƙarar Ganduje Da Wasu Kotu Kan Zargin Almundahanar N4.4bn

October 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.