ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Hadejia Da Sarakunanta (6)

Ci gaba daga makon da ya gabata

by Idris Aliyu Daudawa
2 years ago
Hadejia

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)

Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya

8.Umaru bin Buhari,1863-1865

Bayan rasuwar Buhari a fagen daga ko yaki sai dansa Umaru ya zama Sarkin Hadejia na bakwai lokacin ya na da shekara 18.Ya samu damar hawan karagar mulkin ne ta taimakon Sarkin Arewa Tatagana da Sarkin yakin Hadejia Jaji, wanda shi ne mai fada aji kuma bawa na Buhari. (Taskar Suleiman Ginsau).Daular Usumaniyya ce ta amince da nada shi Sarkin a wani kokarin da ta ke  yi na maido da Hadejia karkashin daular Usumaniyya. Sai dai kuma Sarkin Hadejia Umaru ya yi sarauta ne ta shekara biyu, wani abu daban shekarun na da matukar muhimmanci.Kawunsa Haru yana sha’awar zama Sarkin Hadejia, saboda kuwa  a asirce yana kokarin yadda zai raba Umaru da ci gaba da kasancewa ko zama a matsayin Sarkin ta.Da farko sai da aka fara gamawa da Tatagana da  Jiji,wadanda sune suka fi kowa nuna goyon baya ga Umaru a wani shirin da ake yi na raba shi da sarautar.Da haka ne lokacin da Sarkin Hadejia   Umaru ya fita a tafiyar da ya kan yi ta zuwa Kogin Hadejia abin da ya faru shine sai wasu taga cikin ‘yan tawagar shi suka bar shi , suka kkuma hana shi komawa birnin Hadejia.Daga nan sai Sarkin Hadejia Umaru ya yi murabus zuwa Chamo karkashin masarautar Kano inda ya zauna har karshen rayuwarsa ya mutu a shekara 1920. (Taskar Suleiman Ginsau)

  1. Haru bin Sambo, 1865-1885

Da aka yi nasarar cire Umaru daga Sarautar Hadejia sai Haru (Babba )ya haye kan karagar mulki a matsayin Sarkin Hadejia ya yi shekara 20 yana mulki inda ya kawo sauye- sauye a masarautar Hadejia,ya kara bunkasa Ganuwar zuwa yadda take a halin yanzu.Ya gabatar da mulkinsa inda ya kara daukaka tafarkin addinin musulunci ta hanyar bude makarantun Islamiyya da kuma kiran Malamai wadanda suka san al’amarin musulunci daga sauran masarautu. Bai tsaya a nan ba domin kuwa an samu labarin cewar yana  masana addinin musulunci akan hanyarsu ta zuwa Makka inda yake basu shawarar su zauna a Hadejia saboda sha’awar da yake da ita ta yada addinin musulunci.

Bugu da kari lokacin shi ne aka kara fadadad Masallacin Jumma’ar birnin Hadejia inda  ya kara kasancewa babba.Ta bangaren zamantakewa da bunkasa tattalin arzikin ya tsarin ya ya jawo hankalin ‘yankasuwar kasshen  waje zuwa kasuwannin Hadejia. Ya yi hakan ne ta rage harajin shigowa da wasu kaya.Bayan nan kuma ya yaki wadanda ba musulmi ba wasu wuraren  Kare-Kare da Bade,wannan shi ya yi sanadiyar hada Adiani zuwa masarautar  Hadejia.Hakanan ma  a zamanin  sarautar Haru ne aka kawo karshen yawan zaman Manja da Doya da ake yi tsakanin Hadejia da Gumel  inda aka yi babban yaki a Zaburam  shekarar 1872, a lokacin ne aka kashe Sarkin Gumel  Abdu Jatau. Wannan nasarar ce ta kawo karshen yawan yake- yaken da ake yi tsakanin Hadejia da Gumel. Sakin Hadejia Haru ya mutu a shekarar 1885.(Taskar Suleiman Ginsau)

Hadejia
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Tarihi

Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)

May 30, 2026
Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya
Tarihi

Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya

February 22, 2026
Tarihin Sarkin Zazzau Ja’afaru Dan Isiyaku 1936-1959
Tarihi

Tarihin Sarkin Zazzau Ja’afaru Dan Isiyaku 1936-1959. (2)

January 11, 2026
Next Post
Wani Abun Fashewa Ya Tarwatse A Wata Islamiyya, Ɗalibi 1 Ya Rasu, 10 Sun Jikkata A Kaduna

An Gano Wasu Mutum 14 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.