• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taron BRICS Zai Kawowa Nahiyar Afrika Sabbin Damarmaki

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Taron BRICS Zai Kawowa Nahiyar Afrika Sabbin Damarmaki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin kasar Afrika ta Kudu ta ce, ta yi dukkan shirye-shirye domin karbar bakuncin taron kungiyar BRICS ta kasashe masu samun saurin ci gaban tattalin arziki karo na 15, da zai gudana daga ranar 22 zuwa 24 ga wannan wata. 

A karon farko tun bayan barkewar annobar COVID-19, shugabannin kasashen Brazil da Rasha da India da Sin da kuma Afrika ta Kudu da suka hada kungiyar BRICS, za su yi taro ido da ido, wanda ake ganin zai kasance wata zaburarwa ga kasashe masu tasowa musamman ma nahiyar Afrika da a bana za su karbi bakuncin muhimmin taron.

  • Wang Yi Ya Yi Karin Bayani Kan Hadin Gwiwar Kasashen BRICS Yayin Da Duniya Ke Fuskantar Kalubalen Tsaro

Bisa la’akari da ka’idojin kungiyar BRICS na aiwatar da hadin gwiwa bisa girmama juna da kaucewa tsoma baki da kuma tabbatar da daidaito, BRICS ta gabatar da wani sabon salon hadin gwiwa a duniya, haka kuma ta kasance wata dama da kuma fata ga kasashe masu tasowa da aka dade ana ci da guminsu.

Taken taron na bana “BRICS da Afrika: Hadin gwiwa domin gaggauta samun ci gaba tare, ci gaba mai dorewa da huldar kasa da kasa da dukkan bangarori” na nuni da cewa, BRICS na da burin tafiya da nahiyar Afrika da kuma samar da damarmaki. Idan muka yi duba da kasashen kungiyar, mun san cewa kasashe ne dake samun saurin ci gaba ta hanyar dogaro da kansu da al’ummarsu, haka kuma kasashe ne masu kaunar a gudu tare a tsira tare, musamman kasar Sin dake kokarin ganin an gina duniya mai makoma ta bai daya ga dukkan bil adama.

Yadda kasashe da dama kusan sama da 40 suka bayyana sha’awar shiga kungiyar, ya nuna cewa tana da ma’ana, kuma dama ce da nahiyar Afrika ke bukata musamman a wannan lokaci da ake fuskantar tsaiko a fannonin mu’amalar kasa da kasa. Wannan kungiya za ta ba nahiyar Afrika damar koyon dabarun ciyar da kanta gaba, da hadin gwiwa ta moriyar juna bisa adalci da kuma samun moriyar juna. Nahiyar Afrika na bukatar hadin gwiwa da kasashe irin Sin da Rasha da suka tsaya kai da fata wajen yaki da danniya da babakere. Yadda Afrika ta kudu mai masaukin baki ta gayyaci shugabannin kasashen Afrika zuwa taron, ya bude wata kafa da kasashen za su gabatar da irin albarkatun da suke da shi da bangarorin dake bukatar gogewa da kwarewar wadannan kasashe domin su ci gajiyar abubuwan da suka mallaka ta hanyoyin da suka dace ba na ci da gumi ba. Haka kuma, kasancewar wadannan kasashe masu yanayi da al’umma kamar kasashen Afrika, dama ce ta koyon dabarunsu domin shawo kan kalubalen da suke fuskanta.

Labarai Masu Nasaba

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

La’akari da kasar Sin a matsayin mai ruwa da tsaki a kungiyar BRICS, a ganina, kasashen Afrika ba su da wata matsala da wannan kungiya, domin har kullum kasar Sin kan wuce gaba wajen kare moriyarsu da tallafa musu. Kuma na yi imanin kungiyar BRICS wata kafa ce da za ta hada kan kasashe masu tasowa wajen kai su ga samun ci gaba mai dorewa. Haka kuma za ta taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da a nan gaba, an samu kasashe da dama a duniya masu karfi da wadata, ba wai wasu ’yan tsiraru kadai su yi babakere ba.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mawuyaciyar Tsadar Rayuwa: Shugabar WTO Ta Gana Da Tinubu Domin Lalubo Mafita

Next Post

Abba Gida-Gida Ya Nada Sunusi Oscar A Matsayin Mataimakinsa Akan Masana’antar Kannywood. 

Related

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili
Daga Birnin Sin

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

1 hour ago
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

1 hour ago
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
Daga Birnin Sin

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

5 hours ago
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

7 hours ago
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

7 hours ago
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

24 hours ago
Next Post
Abba Gida-Gida Ya Nada Sunusi Oscar A Matsayin Mataimakinsa Akan Masana’antar Kannywood. 

Abba Gida-Gida Ya Nada Sunusi Oscar A Matsayin Mataimakinsa Akan Masana'antar Kannywood. 

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.