ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taron BRICS Zai Kawowa Nahiyar Afrika Sabbin Damarmaki

by CMG Hausa
3 years ago
BRICS

Gwamnatin kasar Afrika ta Kudu ta ce, ta yi dukkan shirye-shirye domin karbar bakuncin taron kungiyar BRICS ta kasashe masu samun saurin ci gaban tattalin arziki karo na 15, da zai gudana daga ranar 22 zuwa 24 ga wannan wata. 

A karon farko tun bayan barkewar annobar COVID-19, shugabannin kasashen Brazil da Rasha da India da Sin da kuma Afrika ta Kudu da suka hada kungiyar BRICS, za su yi taro ido da ido, wanda ake ganin zai kasance wata zaburarwa ga kasashe masu tasowa musamman ma nahiyar Afrika da a bana za su karbi bakuncin muhimmin taron.

  • Wang Yi Ya Yi Karin Bayani Kan Hadin Gwiwar Kasashen BRICS Yayin Da Duniya Ke Fuskantar Kalubalen Tsaro

Bisa la’akari da ka’idojin kungiyar BRICS na aiwatar da hadin gwiwa bisa girmama juna da kaucewa tsoma baki da kuma tabbatar da daidaito, BRICS ta gabatar da wani sabon salon hadin gwiwa a duniya, haka kuma ta kasance wata dama da kuma fata ga kasashe masu tasowa da aka dade ana ci da guminsu.

ADVERTISEMENT

Taken taron na bana “BRICS da Afrika: Hadin gwiwa domin gaggauta samun ci gaba tare, ci gaba mai dorewa da huldar kasa da kasa da dukkan bangarori” na nuni da cewa, BRICS na da burin tafiya da nahiyar Afrika da kuma samar da damarmaki. Idan muka yi duba da kasashen kungiyar, mun san cewa kasashe ne dake samun saurin ci gaba ta hanyar dogaro da kansu da al’ummarsu, haka kuma kasashe ne masu kaunar a gudu tare a tsira tare, musamman kasar Sin dake kokarin ganin an gina duniya mai makoma ta bai daya ga dukkan bil adama.

Yadda kasashe da dama kusan sama da 40 suka bayyana sha’awar shiga kungiyar, ya nuna cewa tana da ma’ana, kuma dama ce da nahiyar Afrika ke bukata musamman a wannan lokaci da ake fuskantar tsaiko a fannonin mu’amalar kasa da kasa. Wannan kungiya za ta ba nahiyar Afrika damar koyon dabarun ciyar da kanta gaba, da hadin gwiwa ta moriyar juna bisa adalci da kuma samun moriyar juna. Nahiyar Afrika na bukatar hadin gwiwa da kasashe irin Sin da Rasha da suka tsaya kai da fata wajen yaki da danniya da babakere. Yadda Afrika ta kudu mai masaukin baki ta gayyaci shugabannin kasashen Afrika zuwa taron, ya bude wata kafa da kasashen za su gabatar da irin albarkatun da suke da shi da bangarorin dake bukatar gogewa da kwarewar wadannan kasashe domin su ci gajiyar abubuwan da suka mallaka ta hanyoyin da suka dace ba na ci da gumi ba. Haka kuma, kasancewar wadannan kasashe masu yanayi da al’umma kamar kasashen Afrika, dama ce ta koyon dabarunsu domin shawo kan kalubalen da suke fuskanta.

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

La’akari da kasar Sin a matsayin mai ruwa da tsaki a kungiyar BRICS, a ganina, kasashen Afrika ba su da wata matsala da wannan kungiya, domin har kullum kasar Sin kan wuce gaba wajen kare moriyarsu da tallafa musu. Kuma na yi imanin kungiyar BRICS wata kafa ce da za ta hada kan kasashe masu tasowa wajen kai su ga samun ci gaba mai dorewa. Haka kuma za ta taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da a nan gaba, an samu kasashe da dama a duniya masu karfi da wadata, ba wai wasu ’yan tsiraru kadai su yi babakere ba.

 

BRICS
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Abba Gida-Gida Ya Nada Sunusi Oscar A Matsayin Mataimakinsa Akan Masana’antar Kannywood. 

Abba Gida-Gida Ya Nada Sunusi Oscar A Matsayin Mataimakinsa Akan Masana'antar Kannywood. 

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.