ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taron BRICS Zai Kawowa Nahiyar Afrika Sabbin Damarmaki

by CMG Hausa
3 years ago
BRICS

Gwamnatin kasar Afrika ta Kudu ta ce, ta yi dukkan shirye-shirye domin karbar bakuncin taron kungiyar BRICS ta kasashe masu samun saurin ci gaban tattalin arziki karo na 15, da zai gudana daga ranar 22 zuwa 24 ga wannan wata. 

A karon farko tun bayan barkewar annobar COVID-19, shugabannin kasashen Brazil da Rasha da India da Sin da kuma Afrika ta Kudu da suka hada kungiyar BRICS, za su yi taro ido da ido, wanda ake ganin zai kasance wata zaburarwa ga kasashe masu tasowa musamman ma nahiyar Afrika da a bana za su karbi bakuncin muhimmin taron.

  • Wang Yi Ya Yi Karin Bayani Kan Hadin Gwiwar Kasashen BRICS Yayin Da Duniya Ke Fuskantar Kalubalen Tsaro

Bisa la’akari da ka’idojin kungiyar BRICS na aiwatar da hadin gwiwa bisa girmama juna da kaucewa tsoma baki da kuma tabbatar da daidaito, BRICS ta gabatar da wani sabon salon hadin gwiwa a duniya, haka kuma ta kasance wata dama da kuma fata ga kasashe masu tasowa da aka dade ana ci da guminsu.

ADVERTISEMENT

Taken taron na bana “BRICS da Afrika: Hadin gwiwa domin gaggauta samun ci gaba tare, ci gaba mai dorewa da huldar kasa da kasa da dukkan bangarori” na nuni da cewa, BRICS na da burin tafiya da nahiyar Afrika da kuma samar da damarmaki. Idan muka yi duba da kasashen kungiyar, mun san cewa kasashe ne dake samun saurin ci gaba ta hanyar dogaro da kansu da al’ummarsu, haka kuma kasashe ne masu kaunar a gudu tare a tsira tare, musamman kasar Sin dake kokarin ganin an gina duniya mai makoma ta bai daya ga dukkan bil adama.

Yadda kasashe da dama kusan sama da 40 suka bayyana sha’awar shiga kungiyar, ya nuna cewa tana da ma’ana, kuma dama ce da nahiyar Afrika ke bukata musamman a wannan lokaci da ake fuskantar tsaiko a fannonin mu’amalar kasa da kasa. Wannan kungiya za ta ba nahiyar Afrika damar koyon dabarun ciyar da kanta gaba, da hadin gwiwa ta moriyar juna bisa adalci da kuma samun moriyar juna. Nahiyar Afrika na bukatar hadin gwiwa da kasashe irin Sin da Rasha da suka tsaya kai da fata wajen yaki da danniya da babakere. Yadda Afrika ta kudu mai masaukin baki ta gayyaci shugabannin kasashen Afrika zuwa taron, ya bude wata kafa da kasashen za su gabatar da irin albarkatun da suke da shi da bangarorin dake bukatar gogewa da kwarewar wadannan kasashe domin su ci gajiyar abubuwan da suka mallaka ta hanyoyin da suka dace ba na ci da gumi ba. Haka kuma, kasancewar wadannan kasashe masu yanayi da al’umma kamar kasashen Afrika, dama ce ta koyon dabarunsu domin shawo kan kalubalen da suke fuskanta.

LABARAI MASU NASABA

Wakilin Sin: Kar A Bari Sabon Nau’in Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ya Haifar Da Karin Tasiri

CDC Ta Afirka Ta Yaba Da Goyon Bayan Da Sin Ta Bayar Da Hadin Gwiwa Mai Karfi Wajen Yaki Da Ebola

La’akari da kasar Sin a matsayin mai ruwa da tsaki a kungiyar BRICS, a ganina, kasashen Afrika ba su da wata matsala da wannan kungiya, domin har kullum kasar Sin kan wuce gaba wajen kare moriyarsu da tallafa musu. Kuma na yi imanin kungiyar BRICS wata kafa ce da za ta hada kan kasashe masu tasowa wajen kai su ga samun ci gaba mai dorewa. Haka kuma za ta taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da a nan gaba, an samu kasashe da dama a duniya masu karfi da wadata, ba wai wasu ’yan tsiraru kadai su yi babakere ba.

 

BRICS
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Wakilin Sin: Kar A Bari Sabon Nau’in Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ya Haifar Da Karin Tasiri
Daga Birnin Sin

Wakilin Sin: Kar A Bari Sabon Nau’in Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ya Haifar Da Karin Tasiri

June 27, 2026
CDC Ta Afirka Ta Yaba Da Goyon Bayan Da Sin Ta Bayar Da Hadin Gwiwa Mai Karfi Wajen Yaki Da Ebola
Daga Birnin Sin

CDC Ta Afirka Ta Yaba Da Goyon Bayan Da Sin Ta Bayar Da Hadin Gwiwa Mai Karfi Wajen Yaki Da Ebola

June 27, 2026
Firaministan Guinea Ya Yabi Kasar Sin Bisa Shawarwarin Da Ta Gabatar
Daga Birnin Sin

Firaministan Guinea Ya Yabi Kasar Sin Bisa Shawarwarin Da Ta Gabatar

June 27, 2026
Next Post
Abba Gida-Gida Ya Nada Sunusi Oscar A Matsayin Mataimakinsa Akan Masana’antar Kannywood. 

Abba Gida-Gida Ya Nada Sunusi Oscar A Matsayin Mataimakinsa Akan Masana'antar Kannywood. 

LABARAI MASU NASABA

Kofin Duniya

Daga 1930 Zuwa 2026: Yadda Aka Buga Wasa Na Dubu Ɗaya A Gasar Kofin Duniya

June 27, 2026
Wakilin Sin: Kar A Bari Sabon Nau’in Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ya Haifar Da Karin Tasiri

Wakilin Sin: Kar A Bari Sabon Nau’in Ra’ayin Nuna Karfin Soja Ya Haifar Da Karin Tasiri

June 27, 2026
Manoma Sun Nemi Tinubu Ya Kara Yawan Tallafin Noma 

Ko Shirin Da Gwamnatin Jihar Katsina Ke Yi Wa Manoma Zai  Amfane Su A wannan Daminar?

June 27, 2026
CDC Ta Afirka Ta Yaba Da Goyon Bayan Da Sin Ta Bayar Da Hadin Gwiwa Mai Karfi Wajen Yaki Da Ebola

CDC Ta Afirka Ta Yaba Da Goyon Bayan Da Sin Ta Bayar Da Hadin Gwiwa Mai Karfi Wajen Yaki Da Ebola

June 27, 2026
Firaministan Guinea Ya Yabi Kasar Sin Bisa Shawarwarin Da Ta Gabatar

Firaministan Guinea Ya Yabi Kasar Sin Bisa Shawarwarin Da Ta Gabatar

June 27, 2026
Zaben 2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Bayyana Shirinsu Yayin Da INEC Ta Fitar Da Jawalin Zabe

2027: Jam’iyyun Siyasa Sun Yi Maraba Da Hukuncin Kotu Kan Dakatar Da Jadawalin INEC

June 27, 2026
ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya

ADC Ta Yi Allah-Wadai Da Soke Rajistar NDC, Ta Yi Gargaɗi Kan Barazanar Dimokuraɗiyya

June 27, 2026
TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

TCN Ta Sanar Da Ɗaukewar Wutar Lantarki A Kano Da Wasu Jihohi Huɗu

June 27, 2026
Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe

Magoya Bayan Pantami Sun Zargi Ana Musgunawa Gombawa Motors A Gombe

June 27, 2026
Babu Wani Saɓani Tsakanin Osimhen Da Lookman – Ndidi

Babu Wani Saɓani Tsakanin Osimhen Da Lookman – Ndidi

June 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.