• English
  • Business News
Tuesday, October 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taron G7 Ya bar Jaki Yana dukan Teki

by CMG Hausa
2 years ago
G7

A kwanakin baya ne, kungiyar kasashe bakwai mafiya karfin tattalin arziki a duniya wato G7 a takaice, ta gudanar da taronta a birnin Hiroshima na kasar Japan.

Sai dai sabanin abin da ya kamata kungiyar ta tattauna game da abubuwa dake addabar duniya a halin da ake ciki, tare da zakulo hanyoyin magance su, sai ta kauce hanya tana shiga sharo ba shanu, ta hanyar tsoma baki a harkokin cikin gidan kasashe, musamman kasar Sin.

  • Sabon Jakadan Sin A Amurka Ya Bukaci A Dawo Da Huldar Kasashen Biyu Bisa Turba Mai Kyau

Wannan ya sa bangaren kasar Sin ya nuna adawa da yadda kungiyar ta G7 take tsoma baki a harkokin cikin gidanta, da neman bata mata suna, da ma cutar da muradun kasar ta Sin.

Yayin taron na wannan karo, shugabar hukumar gudanarwar kungiyar tarayyar Turai wato EU, Ursula von der Leyen, ta yi wasu kalamai marasa dacewa kan kasar Sin, wannan ya sa bangaren Sin, ya kalubalanci kasashen na G7 cewa, Idan har da gaske kasashen G7 suna maida hankali kan kasashe masu tasowa, to, ya dace su cika alkawarin su ba tare da bata lokaci ba, wato amfani da kaso 0.7 bisa dari na daukacin kudin shigar su a kowace shekara don tallafawa kasashen, da samar wa kasashe masu tasowa jarin dala biliyan 100 a fannin sauyin yanayi a kowace shekara, tare kuma da kara daukar nauyin kasa da kasa, da kara yin abubuwan kirki na zahiri a kasashe masu tasowa. Mu gani a kasa, Wai an ce da kare ana biki a gidansu.

A sanarwar Hiroshima da shugabannin kasashen G7 suka fitar kan kwance damarar makaman nukiliya ma, sun soki manufofin gwamnatin kasar Sin kan makaman nukiliya. Sanin kowa ne cewa, wannan ba shi ne ainihin abin da ya kamata kasashen kungiyar su tattauna ba, dadin dadawa ba kungiyar G7 ce take da ikon tsara ka’idojin hana yaduwar makaman nukiliya na kasa da kasa ba, ma’ana ba ta da hurumin baiwa sauran kasashe umarni a wannan fanni.

LABARAI MASU NASABA

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

A don haka, kamata ya yi kungiyar ta tsaya cikin huruminta na tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar da ma ci gaban duniya baki daya, maimakon zama ‘yar kanzakin wasu kasashe don neman kare muradunsu.

Wannan ya nuna a fili yadda kungiyar G7 baki daya, ta bar Jaki tana dukan Teki, inda ta kauce daga muhimman abubuwan da ya kamata ta tattauna a wannan lokaci da duniya ke fama da manyan kalubaloli da ya dace a kai ga samo bakin zaren warwaresu. Masu iya magana na cewa, kowa ya debo da zafi bakinsa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

October 13, 2025
Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta
Daga Birnin Sin

Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

October 13, 2025
Ana Gudanar Da Taron Masu Mukamin Magajin Gari Na Kasa Da Kasa A Birnin Dunhuang Na Sin
Daga Birnin Sin

Ana Gudanar Da Taron Masu Mukamin Magajin Gari Na Kasa Da Kasa A Birnin Dunhuang Na Sin

October 13, 2025
Next Post
Ana Bukatar Wani Tsarin Cinikin Kasa Da Kasa Mai Adalci Dake Iya Yaki Da Babakeren Dalar Amurka.

Ana Bukatar Wani Tsarin Cinikin Kasa Da Kasa Mai Adalci Dake Iya Yaki Da Babakeren Dalar Amurka.

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa

An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa

October 14, 2025
Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi

Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi

October 14, 2025
Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

October 14, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Jarida A Kan Hanyarsa Ta Zuwa Ɗaukar Horo A Kwara

‘Yan Bindiga Sun Sace Ɗan Jarida A Kan Hanyarsa Ta Zuwa Ɗaukar Horo A Kwara

October 14, 2025
Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan

Zaman Gidan Yari Ya Nuna Min Mutanen Da Ya Kamata Na Yi Hulɗar Siyasa Da Su — Faruk Lawan

October 14, 2025
Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

Majalisa Na Shirin Sauya Lokacin Zaɓen 2027 Zuwa Nuwamba 2026

October 13, 2025
Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

Yajin Aiki: Malaman Jami’a Sun Ce Barazanar ‘Ba Aiki, Ba Biya’ Ba Zata Tsorata Su Ba

October 13, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba

October 13, 2025
Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta

October 13, 2025
NPFL Ta Ci Tarar Kano Pillars ₦9.5m, Ta Rage Mata Maki 3 Da Ƙwallaye 3

NPFL Ta Ci Tarar Kano Pillars ₦9.5m, Ta Rage Mata Maki 3 Da Ƙwallaye 3

October 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.