ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jerin Gwarazan Taurarinmu!

by Leadership Hausa
7 months ago
Taurari

1. Sakamakon tallafa wa al’umma da jari da sauran ayyukan jin kai a dukkanin fadin jihohin kasar nan, kula tare da habaka harkokin ilimi, fasaha da bai wa tsofaffi kulawa ta musamman da kuma taimako iri daban-daban, ya sa Sanata Oluremi Tinubu kasancewa a matsayin Gwarzuwar Shekarar 2025. 

Sanata Oluremi Tinubu: Nuna Tausayi Ga Masu Karamin Karfi

  • Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji
  • Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Gwamna Hope Odidikanwa Uzodimma

ADVERTISEMENT

2. Tsarin mulkinsa, ya kawo sauye-sauye tare da dogaro a kan gaskiya, wanda hakan ya hada da inganta harkokin ilimi, karfafa fasaha, sabunta kayan aiki da kuma sake fasalin tsaro; don sake fasalin hidimar jama’a a matsayin dandalin ci gaba da hadin kai; An zabi Gwamna Hope Odidika Uzodimma Gwarzon Gwamnan Shekarar 2025.

Hope Uzodimma: Sake Gina Jihar Imo Da Hangen Nesa Da Jajircewa

LABARAI MASU NASABA

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

3. A Hangen Nesansa wajen jagorancin al’umma, ya mayar da hankali kan masana’antu, sabunta ababen more rayuwa da kuma gina Dan’adam; domin mayar da Jihar Nasarawa matsayin wata babbar cibiyar zuba jari a Nijeriya da horar da aikin injiniya tare da kyautata jin dadin al’ummar jihar; an zabi Injiniya Abdullahi A. Sule a matsayin Gwarzon Gwamnan Shekarar 2025.

Injiniya Abdullahi Sule: Wanda Ya Fi Yin Fice Kan Harkokin Masana’antu A Duk Fadin Arewa

4. Shugabancinsa ya yi matukar kawo sauye-sauye a Jihar Ekiti, musamman ta hanyar gudanar da mulki na adalci, sabunta ayyukan more rayuwa, karfafa matasa da fadada aikin gona; sakamakon tawali’un da yake da shi da horon da ya samu wajen tafiyar harkokin kudi da gina jama’a tare kuma karfafa al’adun demokuradiyya; ya sa aka zabi Biodun Abayomi Oyebanji a matsayin Gwarzon Gwamnan Shekarar 2025.

Biodun Abayomi Oyebanji: Wanda Ya Kawo Juyin-juya-hali A Jihar Ekiti

5. A sauyin da ya kawo a shugabancinsa, jajircewarsa na kawo ci gaba a fannin tsaro, zuba jari mai yawan gaske a fannin ilimi, kiwon lafiya da sauran ababen more rayuwa; kazalika a kokarinsa na sake mayar da Jihar Zamfara kan turbar zaman lafiya da ci gaba mai dorewa, Dauda Lawal shi ne Gwarzon Gwamnanmu na wannan shekara.

Dauda Lawal: Ceto Zamfara Domin Ci Gaba

6. Ya dukufa wajen mayar da hankali kan manufar da ya sanya gaba, mai taken; “MORE Agenda”, wanda ya sake fasalin tsarin mulkin Jihar Delta ta hanyar zaman lafiya, hadin kai da kuma jajircewa wajen samar da ababen more rayuwa, ilimi, lafiya da kuma gina al’adun jama’a bisa gaskiya, tsantseni a sha’anin harkar kudi ta bangarori da dama; Rt. Hon. Sheriff Oborebwori, shi ne gwarzon gwamnanmu na 2025.

Sheriff Oborebwori: Gwamnan Da Ya Ginu Kan Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Al’umma

7. Saboda kasancewarsa mai sasanta mutane da hada kansu duk da bambance- bambancensu; ga kuma samar da abubuwan more rayuwa a kauyuka, farfado da lamarin kula da lafiyar al’umma, taimaka wa manoma da matasa yadda za su tsaya da kafafunsu; tafiyar da gwamnati ta tausaya wa al’umma, yin biyayya da dokoki, da tunanin yadda gaba za ta yi kyau; shi ya sa aka zabi Sanata Uba Sani a matsayin Gwarzon Gwamnan shekarar 2025.

Sanata Uba Sani: Mai Hada Kan Al’ummar Da Suka Rarrabu

Gwarzon Dan Majalisa Na Shekarar 2025

8. Saboda yadda ya shahara wajen yin doka, wakilci, nuna damuwa da sai abu ya kasance; yadda yake da hazaka, sa ido kan ci gaban inda yake wakilta, da kokarin samar da zaman lafiya, tsarin da ya sa aka samu cimma buri a gyaran tsarin mulki, hadin kan kasa;. Honorabul Benjamin Okezie Kalu, PhD, CFR don haka shi ne dan majalisar shekarar 2025.

Benjamin Okezie Kalu: Wakili A Majalisa Saboda Hadin Kan Kasa, Zaman Lafiya, Da Ci Gaba

Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati Na Shekarar 2025

9. Bisa la’akari da yadda ya tafiyar da sha’anin kawo gyara a lamarin tara haraji, abin da aka aiwatar ta yadda ya dace a yi da gaskiya domin habbaka hanyoyin samun kudaden shiga ba ta hanyar man fetur ba, amma ta hanyar bullo da wasu dabaru ta kafar sadarwa ta zamani; da yake an dauki hukumomin gwamnati da su ma abokan tafiya ne domin samun ci gaba, ba tare da an sa wani abu na matsi ba; Dakta Zacch Adedeji a yanzu shi ne gwarzon ma’aikakaci na shekarar 2025.

Dakta Zacch Adedeji: Wanda Ya Kara Daukaka Darajar Haraji A Nijeriya

Gwarzon Dan Kasuwa Na 2025

10. Saboda hangen nesansa wajen kawo gyara a lamarin bunkasa samar da takin zamani a Nijeriya da kuma harkar kasuwancin amfanin gona; don tallafa wa miliyoyin manoma hanyar amfani da abubuwan gida. Da kuma kokarinsa na samar da wata hanyar taimakawa masu karamin karfi yadda za su cimma burinsu na maida aikin gona a matsayin wata hanya da za ta taimaka wa al’umma; don haka Thomas Etuh shi ne gwarzon Dan kasuwa na shekarar 2025.

Thomas Etuh: Gwarzo Wajen Samar Da Hanyoyin Dogaro Da Kai Ga Matasa

Gwarzon Shugaban Kamfani Na Shekarar 2025

11. Domin jagorantar bangaren hakar mai da iskar gas na tekun Nijeriya da ya yi nasarar samar da ganga miliyan 1.8 na man fetur a kowace rana; da kuma jagorantar hukumar NUPRC ta zarce burinta na samun kudaden shiga da kashi 84.2 cikin dari, Injiniya Gbenga Komolafe shi ne Gwarzon Shugaban Kamfani na Shekara ta 2025.

Gbenga Olu Komolafe: Jagorantar Tsarin Samar Da Makamashi A Nijeriya

Gwarzon Ma’aikacin Banki Na Shekarar 2025

12. Domin jagorantar harkar kudi ta hanyar kirkire-kirkire tare da karfafa samar da kanana da matsakaitan sana’o’i (MSME) 700,000 da karfafa tubalin tattalin arzikin Nijeriya da kuma sake fasalta banki; an zabi Dakta Tony Okpanachi a matsayin Gwarzon Ma’aikacin Banki Na Shekarar 2025.

Dr Tony Okpanachi: Gina Makomar Nijeriya Ta Hanyar Tallafa Wa Kananan Kamfanoni

Wanda Da Ya Fi Tasiri A Kafofin Sada Zumunta Na Shekarar 2025

13. Domin sauya rikici zuwa hadin kai, da tashin hankali zuwa ci gaba mai ma’ana da kirkirar ayyukan yi, samar da zaman lafiya da sabunta zamantakewa, al’adu da tattalin arzikin Neja Delta da zuba jari a ilimi, kiwon lafiya, muhalli da karfafa ci gaba, an zabi Babban Sarki Oweizide Ekpemupolo (Tompolo) a matsayin mafi tasiri a Kafofin Sada Zumunta na 2025.

Babban Sarki Oweizide Ekpemupolo (Tompolo): Hiddimta Wa Al’umma Ba Tare Da Gajiyawa Ba

Gwarzuwar Hukumar Gwamnati Ta Shekarar 2025

14. Domin fadada iyakokin aiwatar da doka a Nijeriya tare da dawo da fiye da naira biliyan 10 ga masu amfani da kayayyaki tare da kalubalantar rashin adalci na kamfanoni da kafa sabbin ka’idoji kula da kasuwanci ta kafafen sadarwar zamani da tabbatar da adalci da shugabanci na na gari — Hukumar Kare ‘Yancin Masu Amfani da Kayayyaki ta Kasa (FCCPC), ita ce Gwarzuwar Hukumar Gwamnati ta Shekarar 2025.

Hukumar Kare ‘Yancin Masu Amfani Da Kaya (Fccpc): Tabbatar Da Adalci A Kasuwa

SkalesShi Ne Gwarzon Mawakin Shekarar 2025

15. Sakamakon tasirin da ya dade yana yi a fannin waka a Nijeriya da kasashen waje. Shahararriyar wakarsa “Shake Body”, wacce ta kai ga samun miliyoyin masu sauraro a Spotify da kuma kwarewarsa a fannin fasahar hada al’umma daban-daban. SKALES ne Gwarzon Mawakin Shekarar 2025.

Kanyenyachukwu Tagbo Okeke Shi Ne Gwarzon Mai Zane Na Shekarar 2025

16. Saboda sanya Nijeriya a taswira ta duniya tare da Guinness World Record (GWR) na Mafi Girman Zanen Canbas da mutum daya ya yi a wannan shekara, da kuma wayar da kan jama’a kan cutar autism a Nijerriya, tare da amfani da fasaha wajen karfafa hadin kai da ilimi ga mutane masu kwarewa daban-daban, Kanyenyachukwu (wanda aka fi sani da Kanye) Tagbo-Okeke shi ne Gwarzon Mai Zane na Shekara 2025.

Gwarzon Mai Koyar Da Wasanni Na Shekarar 2025

17. Saboda jagorantar Super Falcons zuwa nasarar lashe kofin WAFCON karo na 10, wanda ya kara musu tasiri; da nuna kwarewa a dabaru da shugabanci da dawo da aminci a kwallon kafar Nijeriya da kuma karfafa sabon karni na masu horar da kwallo a Afirka, Justine Madugu shi ne gwarzon mai koyar da wasanni na Shekarar 2025.

Justine Madugu: Mai Dabaru Dawo Da Darajar Kwallon Kafa A Nijeriya

Dabid Adeyemi Shi Ne Gwarzon Matashi Na Shekara 2025

18. Dangane da habaka kirkira, tausayi da kwarewa ta hanyar kirkirar manhajar AI wacce ke sauya yadda dalibai masu nakasar gani ke samun ilimi a Nijeriya da wajenta, Dabid Adeyemi shi ne Gwarzon Matashi na Shekarar 2025.

Gwarzon Ma’aikacin Lafiya Na Shekarar 2025

19. Domin ganin yadda ya sauya akalar samar da kiwon lafiya cikin tausayi da soyayya ga mabukata tare da yi wa mutane fiye 2,600 tiyata kyauta a sassan kasar nan. Dr Seidu Adebayo Bello shi ne Gwarzon Ma’aikacin Kiwon Lafiya na shekarar 2025.

Dr Seidu Adebayo Bello: Ya Dawo Da Fata Ga Al’umma

Misis Mabel Ijeoma Duaka Shi Ne Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025

20. Duk da ayyukan ta’addanci na Boko Haram, yayin da al’umma musamman baki ke gudu daga yankuna da dama na Jihar Borno, ta gwammace ta zauna a karamar hukumar Mafa domin ci gaba da bayar da kulawa ga wadanda suka jikkata na tsawon shekara 21. Mrs Mabel Ijeoma Duaka ce Gwarzuwar Ma’akaciyar jinya ta shekarar 2025

Bankin Probidus Ne Gwarzon Banki Na Shekarar 2025

21. Saboda kasancewa kan gaba wajen zamanantar da harkokin Banki a Nijeriya da kuma karfafa wa manya da kananan masa’na’antu tare da zama a kan gaba wajen daukaka darajar aikin Banki a Nijeriya, Bankin Probidus ne Gwarzon bankinmu na shekarar 2025.

Gwarzuwar Matashiya ‘Yar Makaranta Ta Shekarar 2025

22. Domin nasarar da ta samu wajen sanya sunan Nijeriya a fagen ilimi a duniya da jajircewa, hazaka da bayar da shawarwari don zaburar da sabbin dalibai don rungumar harshe Turanci da tabbatar da nasara na iya tasowa daga kowane bangare. An bai wa Nafisa Abdullahi Aminu lambar yabo ta Gwarzuwar Matashiyar 2025.

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Daukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

Hukumar NASENI Ne Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025

23. Domin yadda ta jagoranci ci gaban masana’antu, samar da makamashi, da fasahohin da suka dace da yanayin da ke rage fitar da iskar carbon mai guba da inganta hanyoyin samar da wutar lantarki mai tsabta; karfafa masu kirkire-kirkire na cikin gida, samar da dabarun tattalin arzikin mai dorewa, da habaka dogaro da kai a Nijeriya ta hanyar bincike da kula da muhalli, Hukumar NASENI ce Gwarzuwar Hukumar da ta fi tasiri wajen kare muhalli a shekarar 2025.

Gwarzon Kamfanin Fasahar Kudade Na Shekarar 2025

24. Don kawo sauyi a harkokin kudade ta hanyar fasahar zamani da suka hada da kirkira da gaskiya wajen karfafa miliyoyin ‘yan Nijeriya, kanana da matsakaitan kamfanoni (MSME) ta hanyar amfani da wayar hannu, don kawo karshen matsalolin kudade ta hanyar fasahar zamani, OPay Nigeria ya amsa sunansa na zama gwarzon kamfanin fasahar harkokin kudade na shekarar 2025.

OPay Nigeria: Tabbatar Da ‘Yancin Hada-hadar Kudi

Kamfanin GEIL: Gwarzon Kamfanin Samar Da Kayayyakin Gida Na Mai Da Gas Na Shekarar 2025

25. Domin jagorantar bunkasawa da gudanar da tashar fitar mai na farko a Nijeriya fiye da shekaru 50, Kamfanin GEIL shi ne Gwarzon Shekarar 2025

Gwarzon Kamfanin Samar Da Kaya Na Shekarar 2025

26. Domin habaka samar da ruwan sha mai inganci da arha, dandano da wayar da kan ‘yan kasa kan amfani da tsaftataccen ruwa, kamfanin Nestlé Pure Life Nigeria Plc shi ne gwarzon samar da kaya a shekarar 2025.

Kamfanin Nestlé Pure Life: Tsarinsa Da Manufa

Kamfanin Trade Modernisation Project: Gwarzon Kamfani Na Shekarar 2025

27. Domin sauya tsarin kasuwancin Nijeriya ta hanyar fasahar zamani da inganci, sarrafa ayyuka, kara habaka samun kudaden shiga da saukaka gudanar da kasuwanci, bunkasa hadin gwiwar gwamnati da masu zaman kansu, samar da ayyukan yi da karfafa gasa, Kamfanin Trade Mo

dernisation Project (TMP) shi ne gwarzon Kamfanin shekarar 2025.

Taurari
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe

MASU ALAKA

Taurari
Rahotonni

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

May 17, 2026
Taurari
Rahotonni

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

May 16, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Rahotonni

Almajiranci:Matsala Ko Maslaha

May 10, 2026
Next Post
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.