• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taron Wayar Da Kan Manema Labarai Kan Alluran Da Ba Su Da Nasaba Da Foliyo

by Sulaiman
3 years ago
in Siyasa
0
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

Shugaban sashen hulda da jama’a na hukumar kula da lafiya matakin farko ta kasa Muhammed Okitoto, ya yi wa mahalarta taron,da aka yi a dakin taro na NAF Conference Centre Abuja jawabin barka da zuwa.
Ya ce su alluran rigakafi da basu da nasaba da cutar Polio wani tsari ne daga sashen da yake kula da al’amuran da suka shafi Bakondauro da dai sauran wadansu cututtuka, na daga cikin ayyukan da ake yi, shi tsarin yana da matukar muhimmanci ga ita hukumar, domin manema labarai sune wadanda suke sada su da al’ummar da take yin ayyukan saboda su.
Ya ci gaba da bayanin cewa duk wadansu ayyukan da ake yi a hukumar ana yin su ne saboda al’ummar Nijeriya, da suka kunshi manya da kananan yara.Don haka yana da kyau su manema labarai su fahimci al’amarin da ake magana kan sa, wato abinda ita hukumar take bukata domin idan za su sanar da al’umma su fada masu gaskiyar yadda al’amarin ya ke.
An shirya shi ne saboda Editoci da sauran marubuta labaran da suka shafi kiwon lafiya.Ya kara da cewa akwai abubuwan da yawa wadanda za ayi musamman ma alluran rigakafin da basu da nasaba da cutar Polio, don haka ake bukatar hadin kan su manema labarai.
Njideka Oshioke ita ta yi karin haske kan dalilin da yasa aka kira taron inda ta ce daga karshen taron wayar da kan manema labarai ana sa ran,za su san wuraren da za a yi su alluran rigakafin da basu nasaba da cutar Polio.
Bugu da kari kuma a san shi matakin da hukumar ta dauka kan allurar rigakafi na cutar Korona. Akwai tabbacin da ake da shi na sa ran,su mahalarta taron za su san dalilan da suka sa aka kira taron dangane da alluran da basu alaka da Polio.
Ita kuma Dokta Maimuna Hamisu ta yi jawabin ta ne kan alluran da hukumar lafiya matakin farko ta kasa tayi shirin aiwatarwa a 2021 amma ba a samu damar yin su ba kamar yadda yakamata ba, shi yasa ahar abin ya fado zuwa 2022.an yi shirin yi ma yara allurar rigakafin da ba ta da nasaba da cutar Polio,wani karamin sashe ne dake karkashin sashen kawar da cututtuka shi ne ya shirya yin alluran.
Babbar manufar sashen ne ya shirya da kuma aiwatar da alluran rigakafi wadanda bata shafi Polio ba,a cikin kasa Nijeriya da kuma wasu bangarori nata.
Da akwai kuma kai taimakon gaggawa wanda ya shafi barkewar wata cuta,a ko wanne bangare na kasa abin ya faru, wannan kuma yana daidai da ayyukan shi sashen, an yin alluran rigakafin cututtukan da za a iya maganinsu,wato kamar Kyanda,Shawara,Sankarau,da kuma sauran cututtukan da allurar rigakafi zata iya maganinsu.
Ta yi a bayanai kan yadda cututtakan su ke alal misali cutar Kyanda wadda take addabar kananan yara masu shekara biyar, da duk yadda ake kamuwa da su.Har ma lokacin da ake kamuwa da su,lokacin da ake wadannan alluran shi ne a watanni hudu na karshen shekara kamar yadda ta jaddada.
Manufar domin daga watan Satumba zuwa Disamba wannan lokacin ne ya fi dacewa a bada gudunmawa, domin cututtukan basu yaduwa a irin yanayin.Jihohi ashirin da biyar da suka hada da babban birnin tarayya na iya kamuwa da cutar Sankarau.An dauki matakan da suka kamata ta hanyar yin alluran har sau hudu, an yi ma masu shekaru daban- daban da aka yi ma yaran da ba samu damar yi masu alluran rigakafin ba, da aka yi a baya.Inda kuma tace tun daga wancan lokacin kuma ba a kara samun wani labarai barkewar cutar ta Sankarau ba.
Ba kuma kamar yadda aka saba ba a shekarun baya wannan karo Jihohi ma za su bada ta su gudunmawar ta kudi,domin aiwatar da shi tsarin na alluran rigakafi na cututtukan da basu nasaba da Polio.Yaran da za ayi ma allurar rigakafin Sankarau wannan shekarar su ne wadanda ba a samu damar yi masu bane tsakanin shekarun 2011 da 201,wannan kuma yaran da za ayi mawa sune wadanda ba a haifa ba tsakanin shekarun. Har ila yau, ta ce Nijeriya tare da hadin kan hukumar lafiya ta duniya sun kaddamar da wani shiri na kawo dauki kan maganin cutar Shawara,a shekarar 2018, kudurin da ake da shi shi ne a gama da cutar Shawara nan da shekara ta 2026.
Daga karshe manema labara ko ‘yanjarida an yi kira da su cewa duk wani labarin da suka samu, ba sai sun yi gaggawar buga shi ba a Jarida,ko amfani da shi a gidajen Rediyo da Talbijin.Babban abinda ya dace su yi shi ne suke yin bincike don gane gaskiyar al’amarin kafin su kai ga bugawa, musamman ma kamar al’amarin daya shafi kiwon lafiya.
Shi Komai gaskiya da gaskiya labarin kiwon lafiya ne ake bukata, ba wata kumbiya- kumbiya,hukumar lafiya matakin farko ta kasa tana aiki kafada kafada da kafofin yada labarai, saboda ta hanyar ce suke sanar da al’umma halin da ake ciki dangane da al’amarin kiwon lafiya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kisan ‘Yan Arewa A Kudu: An Bukaci Gwamnati Ta Gaggauta Daukar Mataki

Next Post

Manyan Kurakuren Iyaye Wajen Tarbiyya (II)

Related

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki
Manyan Labarai

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

4 days ago
Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike
Siyasa

Babu Wanda Zai Iya Kora Ta Daga PDP —  Wike

5 days ago
Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya
Siyasa

Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

1 week ago
‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027
Siyasa

‘Aikin Yan Uba Ne’ — Yahaya Bello Ya Karyata Zargin Sha’awar Takarar Shugaban Kasa A 2027

2 weeks ago
Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi
Labarai

Sanata Adamu Aliero Ya Ƙaddamar Da Rabon Kayan Tallafi Ga Ƙananan Hukumomi Takwas A Kebbi

2 weeks ago
PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe
Siyasa

PDP Ta Sake Zaɓar Amb. El-Gash A Yobe

3 weeks ago
Next Post
Manyan Kurakuren Iyaye Wajen Tarbiyya (II)

Manyan Kurakuren Iyaye Wajen Tarbiyya (II)

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.