ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Kurakuren Iyaye Wajen Tarbiyya (II)

by Sulaiman
4 years ago

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Assalamu Alaikum! Barkanmu da sake kasancewa da ku a cikin wannnan shiri wanda muke zabo batu (Topic) duk mako dan tattaunawa a kansu. A wannan makon za mu tattauna ne a kan KURAKUREN IYAYE YAYIN TARBIYYA. Tabas! Sau tari musamman a irin zamanin da muke ciki iyaye na sakaci sosai wajen tsayawa gun ba ‘ya’yayensu tarbiya, kama daga kan Uba zuwa kan Uwa.

Sakacin Iyaye Maza: A wannan zamanin Maza da yawa za ka iya samu ba su san me ake a gidansu ba musamman ‘ya’yayensu. Gaba daya za ka tarar ya sake ma Mace tarbiyar da kulawa da yaran, wani idan ya sa kai ya fice tun safe ba za ka kuma ganinsa ba sai dare, lokacin za ka iya tararwa yaran sun yi bacci, idan ma idonsu biyu shi din ya gaji bai da lokacin da zai zauna ya kula da abin da ke tafiya a cikin gidansa ko da na mintuna ne kuwa. Abin da suka sani shine idan yaro ya yi mara kyau su danganta da uwa da rashin zamansu sun manta da kiwo ne Allah ya dora a wuyansu.
Mace ce ginshikin tarbiyar yara wanda shi ya sa ake cewa idan za ka yi Aure ka auro ma ‘ya’yayenka Uwa tagari, sai dai hakan ba yana nufin ka sake ma mace ragamar komai na tarbiya ba ne dole tana bukatar mataimaki musamman yaranmu na zamani masu zuwa da wayau sosai dole sai iyaye biyu sun yi tsayuwar daka gun kulawa. An sani Namiji shi ke fita gwagwarmaya wajen nema domin iyalansa. Sai dai yana da kyau har ila yau a ce ya ware lokuta na musamman wajen kulawa da su idan ba haka ba, zai gama neman kudinsa bayan shekaru ya tsinci yaransa wasu iri ba yadda ya so ba, ma’ana tarbiyar ta lalace ko wani abu wanda ba zai taba jindadin hakan ba. Wannan kenan. A cikin al’kur’ani maigirma Suratul Attahrim Aya ta 6. Allah (SWT) yana cewa, “yaku wadanda kukayi Imani! Ku kare kanku da iyalanku daga wuta makamashinta mutane da duwatsu ne. A kanta akwai wasu mala’iku masu kauri, masu karfi. Ba su saba wa Allah ga abin da ya umarce su, kuma suna abin da ake umarninsu”. Allah yaba mu ikon kulawa Ameen.
Sakacin Iyaye Mata: wajibi ne duk Uwa tagari ta yi wa yaranta tarbiyya tagari dan su zamanto na gari. Tarbiya ita ce gatan da iyaye za su iya ma ‘ya’yansu wanda zai zama tsaninsu kan addini da zamantakewa cikin al’umma. Zamani Allah ya kawo mu inda za ka tarar waya da ‘social media’ ya fi ma wata Uwar yaranta, wata ko me yaron yake ba ruwanta, haka a kan waya ma wata sai ta kora yaran da cewan sun dame ta ba ruwanta da matsalar yaran ko da a makaranta an musu wani abun zai yiwu ‘information (bayani)’ ne me ma’ana ya kawo ta kore shi. Yau da gobe da na zuwa ana korar shi har zai gaji ya daina kokarin kawo wa uwar lalurarsa ko da ana mishi wani mugun abun da ya kamata ta ankara tun da ba maida hankali ta yi wajen lura da su ba bare ya dame ta, abin da ta sani kawai ta dafa ta ba su su ci shikenan. Wata ko wankansu da tsafta ba ruwansa ba ta gyara kanta ba 24/7 tana ‘social media’ bare ta gyara su.
Ire-iren haka ne sai kaji ana ta bata yarinya ko yaro tsawon lokaci in ba abin ya yi tsamari ko ya zo da matsala ba, ba a taba sani ko ka ji an sani a lokacin da bakin alkalami ya bushe, ma’ana lokaci ya kure. In ka zo bangaren yara mata za ka samu wasu Matan sai ka ga ‘yar yarinya ta yi ‘toilet’ tana ta magana “na gama” kuma ita ba ta kai wanke ma kanta ba amma sai ka samu wannan uwar na zaune, abun ba zai ba ka mamaki ba sai ta soma kiran yayyun wannan yarinyar tata maza su wanke mata, wani ma kila dan dan’uwan ne ko kanin ita wannan uwar ko dan uwan uban. Kai wani lokaci ma sai dai Uban ya fita da kansa ya yi wannan aikin.

Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
  • Sulaiman
    Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba
  • Sulaiman
    Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Next Post
Yadda Uwargida Za Ta Hada Kayan Makolashe

Yadda Uwargida Za Ta Hada Kayan Makolashe

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.