• English
  • Business News
Friday, May 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tashar Lekki Ta Sa Kaimin Bunkasuwar Tattalin Arzikin Yammacin Afirka

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Lekki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yau ina tare da wani albishirin da zan so in gutsura muku. Tashar jiragen ruwa ta Lekki da ke birnin Lagos, ta riga ta samar da guraben aiki sama da 3,000 ga al’ummar wurin tun bayan da ta fara aiki a hukunce a watan Afrilun wannan shekara.

An ce, tashar Lekki na iya samar da guraben aiki kimanin dubu 170, kuma sama da kaso 90% daga cikinsu an samar da su ne ga mazauna wurin.

  • Manoman Kenya Na Kara Rungumar Fasahohin Inganta Noma Na Sin
  • An Yabawa Ci Gaban Jamhuriyar Jama’ar kasar Sin Yayin Liyafar Da Aka Shirya Domin Murnar Cikarta Shekaru 74 Da Kafuwa 

Har wa yau, kasancewarta tasha mai zurfin ruwa ta zamani irinta ta farko a Nijeriya, wadda kuma ke daya daga cikin tashoshi masu zurfin ruwa mafiya girma a yammacin Afirka, yadda aka fara aiki da tashar Lekki, ya daidaita matsalolin koma bayan ababen tashar Lagos da ke yi wa ci gaban cinikin da Nijeriya ke yi da kasa da kasa tarnaki, wadda ta yi matukar kyautata kwarewar birnin Lagos ta fannin shige da ficen hajjoji.

Ban da haka kuma, sakamakon yadda Nijeriya ta kasance kofar wasu kasashen da ke cikin Afirka, irinsu Chadi, da Nijer ta hadewa da teku, tashar ta Lekki, za ta kuma kara samar da karfin bunkasuwar tattalin arzikin shiyyar.

Hadewa da juna ta bangaren manyan ababen more rayuwa, na daya daga cikin manyan burikan da ake neman cimmawa wajen aiwatar da shawarar ziri daya da hanya daya, a wani kokari na sa kaimin bunkasuwar tattalin arzikin shiyya, da ma na duniya baki daya. Kasancewarsa daya daga cikin nasarorin da aka cimma a gun taron kolin kasa da kasa karo na biyu kan shawarar ziri daya da hanya daya, tashar Lekki ba kawai ta taimaka ga ci gaban tattalin arzikin cikin gidan Nijeriya ba ne, har ma za ta zama muhimmiyar mahada ta teku, wanda hakan ya aza ingantaccen harsashi ga bunkasuwar tattalin arzikin Afirka baki daya. (Mai Zane:Mustapha Bulama)

Labarai Masu Nasaba

An Gudanar Da Dandalin Kawancen Birane Na Kasa Da Kasa Na Shanghai 

Darajar Sashen Masana’antun AI Na Sin Ta Kai Kusan Yuan Biliyan 600

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: PacificTashar ruwaTekun Legas
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Uba Sani Ya Taya Sarkin Zazzau Murnar Cika Shekara Uku A Kan Karagar Mulki 

Next Post

2034: Nijeriya Na Goyon Bayan Saudiyya Ta Dauki Nauyin Kofin Duniya

Related

An Gudanar Da Dandalin Kawancen Birane Na Kasa Da Kasa Na Shanghai 
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Dandalin Kawancen Birane Na Kasa Da Kasa Na Shanghai 

9 hours ago
Darajar Sashen Masana’antun AI Na Sin Ta Kai Kusan Yuan Biliyan 600
Daga Birnin Sin

Darajar Sashen Masana’antun AI Na Sin Ta Kai Kusan Yuan Biliyan 600

9 hours ago
Sanarwar Bayan Taron Kolin Sin Da ASEAN Da GCC Ta Yi Nuni Ga Burin Kara Dunkulewa Waje Guda
Daga Birnin Sin

Sanarwar Bayan Taron Kolin Sin Da ASEAN Da GCC Ta Yi Nuni Ga Burin Kara Dunkulewa Waje Guda

11 hours ago
Sin Ta Cimma Nasasar Harbar Na’urar Nazarin Tauraro a Sararin Sama Mai Lakabin “Tianwen-2”
Daga Birnin Sin

Sin Ta Cimma Nasasar Harbar Na’urar Nazarin Tauraro a Sararin Sama Mai Lakabin “Tianwen-2”

11 hours ago
AU Ta Jinjinawa Goyon Bayan Sin Ga Ci Gaban Nahiyar Afrika
Daga Birnin Sin

AU Ta Jinjinawa Goyon Bayan Sin Ga Ci Gaban Nahiyar Afrika

13 hours ago
Sin Da Kasashen Yankin Pasifik Sun Yi Nasarar Gudanar Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Karo Na Uku
Daga Birnin Sin

Sin Da Kasashen Yankin Pasifik Sun Yi Nasarar Gudanar Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Karo Na Uku

13 hours ago
Next Post
2034: Nijeriya Na Goyon Bayan Saudiyya Ta Dauki Nauyin Kofin Duniya

2034: Nijeriya Na Goyon Bayan Saudiyya Ta Dauki Nauyin Kofin Duniya

LABARAI MASU NASABA

Gasar Wasanni Ta Kasa Wata Hanya Ce Ta Hada Kan Matasan Nijeriya– Obasanjo

Gasar Wasanni Ta Kasa Wata Hanya Ce Ta Hada Kan Matasan Nijeriya– Obasanjo

May 29, 2025
An Gudanar Da Dandalin Kawancen Birane Na Kasa Da Kasa Na Shanghai 

An Gudanar Da Dandalin Kawancen Birane Na Kasa Da Kasa Na Shanghai 

May 29, 2025
Darajar Sashen Masana’antun AI Na Sin Ta Kai Kusan Yuan Biliyan 600

Darajar Sashen Masana’antun AI Na Sin Ta Kai Kusan Yuan Biliyan 600

May 29, 2025
Yadda Rikici Ya Yi Sanadin Kashe DPO A Kano

‘Yansanda Sun Kama Mutane 41 Da Ake Zargi Da Kisan DPO A Kano

May 29, 2025
Sanarwar Bayan Taron Kolin Sin Da ASEAN Da GCC Ta Yi Nuni Ga Burin Kara Dunkulewa Waje Guda

Sanarwar Bayan Taron Kolin Sin Da ASEAN Da GCC Ta Yi Nuni Ga Burin Kara Dunkulewa Waje Guda

May 29, 2025
Sin Ta Cimma Nasasar Harbar Na’urar Nazarin Tauraro a Sararin Sama Mai Lakabin “Tianwen-2”

Sin Ta Cimma Nasasar Harbar Na’urar Nazarin Tauraro a Sararin Sama Mai Lakabin “Tianwen-2”

May 29, 2025
Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja

Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja

May 29, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa

‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa

May 29, 2025
AU Ta Jinjinawa Goyon Bayan Sin Ga Ci Gaban Nahiyar Afrika

AU Ta Jinjinawa Goyon Bayan Sin Ga Ci Gaban Nahiyar Afrika

May 29, 2025
Sin Da Kasashen Yankin Pasifik Sun Yi Nasarar Gudanar Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Karo Na Uku

Sin Da Kasashen Yankin Pasifik Sun Yi Nasarar Gudanar Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Karo Na Uku

May 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.