• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tasirin Cibiyar Raya Noma Da Sin Ta Gina A Najeriya

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Tasirin Cibiyar Raya Noma Da Sin Ta Gina A Najeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A farkon makon nan ne gwamnatin Sin ta mikawa gwamnatin Najeriya sabuwar cibiyar binciken harkokin noma, wadda aka kammala ginin ta a garin Bwari dake kusa da birnin Abuja fadar mulkin kasar. Cibiyar dai daya ce daga ayyuka daban daban da kasar Sin ke tallafawa gudanarwa a Najeriya, a wani bangare na cika alkawarun da Sin din ta jima tana dauka, na agazawa abokan tafiyar ta wato kasashe masu tasowa.

Masana sun tabbatar da cewa, wannan cibiya ta bincike, za ta taka muhimmiyar rawa wajen bunkasa, da fadada ci gaban ayyukan noma a kasar mafi yawan jamaa a Afirka. Ko shakka babu, wannan cibiya za ta yi babban tasiri ga alummar Najeriya, musamman manoma, da hukumomin kasar masu nasaba da harkokin noma, da ma matasa wadanda a nan gaba za su samu zarafin shiga sanaar noma gadan gadan.

  • Cinikayyar Waje Ta Hajojin Sin Ta Karu Da 8.6% Tsakanin Janairu Zuwa Nuwamba

Mafiya yawa daga mazauna birane musamman matasa dake son fara sanaoi a Najeriya, ba su cika rungumar sanaar noma ba, duba da wahalhalun dake tattare da sanaar, ga kuma karancin dabarun zamani na gudanar da sanaar wanda kan haifar da karancin ribi, ko fuskantar asara yayin da ake gudanar da ita bisa salon gargajiya.

Sabuwar cibiyar dai na kunshe da abubuwa na binciken fasahohin zamani da ake amfani da su a harkar noma, da wuraren ba da horo ko samun kwarewar makamar aiki. Kaza lika ta kunshi kayan aiki na nazari domin saukaka noma a zamanance, ta yadda manazarta za su samu damar zakulo dabaru na sauya akalar ayyukan noma daga na gargajiya zuwa na zamani, da fito da dabarun bunkasa yawan hatsi da manoma za su iya nomawa a Najeriya, da ma fadada sassan noma da kiwo daban daban. Har ila yau, akwai dakunan gwaje gwaje, da madatsar ruwa, da cibiyar nune-nunen yadda ake sarrafa amfanin gona, da cibiyar samar da makamashi da sauran su.

Hakika wannan sabuwar cibiya, shaida ce dake nuni ga manyan nasarori da Sin tare da Najeriya suke samu, karkashin dadadden hadin gwiwa, da zumuncin dake tsakanin sassan biyu.

Labarai Masu Nasaba

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Tabbas, bisa abubuwan da aka tanada a wannan cibiya, yan Najeriya musamman manoma, za su ci babbar gajiya daga fasahohin zamani na bincike da gwaje gwaje, kuma cibiyar za ta ci gaba da zama wata alama, game da kyakkyawar dangantaka dake tsakanin Sin da Najeriya cikin tsawon lokaci. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

A Shirye Nake Don Yin Muhawara Tun Daga Safe Har Zuwa Dare – Tinubu

Next Post

Zulum Ya Gabatar Da N234.8b A Matsayin Kasafin 2023 Ga Majalisar Dokokin Borno

Related

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

17 minutes ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

2 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

3 hours ago
Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Shugabannin Sin Da Amurka Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

14 hours ago
Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

19 hours ago
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

19 hours ago
Next Post
Zulum Ya Gabatar Da N234.8b A Matsayin Kasafin 2023 Ga Majalisar Dokokin Borno

Zulum Ya Gabatar Da N234.8b A Matsayin Kasafin 2023 Ga Majalisar Dokokin Borno

LABARAI MASU NASABA

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

June 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

June 6, 2025
Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

Sallar Layya: Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci Musulmin Su Tuna Da Muhimmancin Sadaukarwa Da Halin Ƙwarai

June 6, 2025
Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

Tsohon Babban Alƙalin Nijeriya  Mohammed Uwais Ya Rasu Ya Shekara 89

June 6, 2025
Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

Wajibi A Mayar Da Hankali Kan ‘Yancin Yara

June 6, 2025
Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

Tsadar Rayuwa: Yadda Al’umma Suka Yi Sallah Cikin Kunci

June 6, 2025
aure

Kar Ki Bari Naman Sallah Ya Kashe Miki Aure Yar’uwa

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.